Zakuna goma sun mutu a wani gandun dabbobi da ke Tanzania

Hukumomi sun ce sakamakon binciken farko ya nuna cewa zakunan sun mutu ne bayan sun “ci guba”, yayin da aka ce ana ci gaba da gudanar da binciken ƙwararru “domin gano musabbabin lamarin da kuma gano waɗanda ke da alhakin aikata hakan”.

Newstimehub

Newstimehub

20 Sep, 2026

dfc1f354 ce94 4e71 9bbb 4aa302e1d3e8 1789887279013

An gano zakuna goma sun mutu a inda ake zargin guba ce ta kashe su a gandun daji na Ngorongoro wanda wuri ne da Hukumar Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta sanya cikin jerin wuraren kare dabbobi na duniya, a cewar hukumomi.

“Hukumar Kula da Yankin Ngorongoro (NCAA) na baƙin cikin sanar da jama’a cewa an gano zakuna goma (10) sun mutu a ranar 18 ga Satumba, 2026, a yankin Ndutu,” in ji sanarwar hukumar da aka fitar a ranar Asabar.

Hukumomi sun ce sakamakon binciken farko ya nuna cewa zakunan sun mutu ne bayan sun “ci guba”, yayin da aka ce ana ci gaba da gudanar da binciken ƙwararru “domin gano musabbabin lamarin da kuma gano waɗanda ke da alhakin aikata hakan”.

Ƙaruwar jama’a

Ngorongoro ya kasance wurin da aka daɗe ana samun rashin jituwa tsakanin hukumomi da al’ummar makiyaya da ke yankin. A wasu lokuta rikicin yakan kai ga rasa rayuka tun bayan da gwamnatin Tanzaniya ta ƙaddamar da shirin korar wasu mazauna yankin a shekarar 2022.

Gwamnatin Tanzaniya ta ce ƙaruwar yawan jama’a na jawo ƙara kutsawa cikin wuraren da namun daji ke rayuwa, inda adadin mutanen da ke zaune a Ngorongoro ya ƙaru daga kusan 8,000 a shekarar 1959 zuwa fiye da 100,000.

Tun watan Yuni, aƙalla giwaye 20 ne suka mutu a tsarin muhalli na Amboseli da ke Kenya, kusa da kan iyakar Tanzaniya, sakamakon zargin gubar maganin kashe ƙwari, ko da yake hukumomi ba su iya tabbatar da ko mutuwar ta faru ne bisa kuskure ko kuma da gangan ba.