Nijeriya ta ƙaddamar da tsarin tattalin arzikin halal domin bunƙasa arzikin ƙasar

Mataimakin shugaban ƙasar Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Tinubu, ya bayyana cewa tsarin zai mayar da hankali kan faɗaɗa fitar da abinci mai bin ƙa’idar halal, bunƙasa masana’antar magunguna da kayan kwalliya da inganta yawon buɗe ido na halal.
6 Feb, 2026
Kotu ta umarci Birtaniya ta biya diyyar £420m ga iyalan masu haƙar kwal 21 a Nijeriya

Alƙalin ya ce nauyi ne da ya rataya kan Gwamnatin Nijeriya a ƙarƙashin sashe na 19(d) da sashi na 150(1) na tsarin mulki ta bi wa mutanen haƙƙoƙinsu, kuma daɗewa da ta yi b ata ɗauki mataki ba wasa da aiki ne.
6 Feb, 2026
NCC ta gargaɗi masu gini da aikin hanya kan lalata layukan sadarwa na ƙarƙashin ƙasa a Nijeriya

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, NCC da NSCDC sun bayyana layukan sadarwan na ƙarƙashin ƙasa a matsayin muhimman kadarorin ƙasa, waɗanda ke tallafa wa tattalin arzikin fasahar zamani na Nijeriya da harkokin kasuwanci.
5 Feb, 2026
Jamhuriyar Benin da AU sun yi Allah wadai da harin ta’addanci da ya kashe mutum 170 a Nijeriya

Tarayyar Afirka ta ce harin “abin ban tsoro da rashin imani” ne; yayin da ita ma Jamhuriyar Benin ta mika ta’aziyya ga Nijeriya.
5 Feb, 2026

Tinubu ya bayar da umarnin tura bataliyar soji Jihar Kwara

Mummunan harin ta’addanci ya kashe fiye da mutum 160 a Jihar Kwara ta Nijeriya

Rundunar sojin Amurka tabbatar da tura ‘wata ƙaramar tawaga’ Nijeriya

‘Yan fashin daji sun kashe mutum 30 a hare-haren da suka kai a Katsina da Kwara

Kotun Najeriya ta tuhumi tsohon ministan shari’a Malami da laifukan ta’addanci
2 Feb, 2026
An gurfanar da mutum 9 a kotu bisa zargin kisan mutum 150 a Yelwata na jihar Benue a 2025
Masu gabatar da karar sun ce hare-haren sun rusa gidaje da dama tare da haifar da asarar rayuka mai yawa a Yelwata da ke gundumar Guma ta jihar Benue.

2 Feb, 2026
Gomman masu ibada da ake fargaba an yi garkuwa da su daga cocin Kurmin Wali sun koma gida
Kamfanin dillancin labaran AFP ya ambato shugaban yana cewa ana tunanin cewa 86 daga cikinsu suna hannun masu garkuwa da mutane kawo yanzu.

1 Feb, 2026
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan Boko Haram, Abu Khalid a Sambisa
Abu Khalid, wanda shi ne mataimakin shugaban Boko Haram na biyu a Dajin Sambisa, an kashe shi tare da wasu ’yan ta’adda 10 yayin wani farmaki da aka kai da dare a Jihar Borno.

31 Jan, 2026
Sojojin Nijeriya sun kashe wani babban kwamandan ISWAP a arewa maso gabas
A cikin wata sanarwar manema labarai, jami’an watsa labarai na rundundar, Laftanar Kanar Sani Uba, ya ce bayanan sirri sun tabbatar da kisan Julaibib, wani babban kwamandan ISWAP da ke aiki a yankin Gujba na abin da ake kira Timbuktu Triangle.

29 Jan, 2026
Nijeriya da Saudiyya sun sanya hannu kan yarjejeniyar ɗaukar ma’aikata a karon farko
Yarjejeniyar na nuna da wani sauyi mai muhimmanci a yadda ma’aikatan Nijeriya ke shiga cikin tattalin arzikin yankin Gulf, daga tsarin hijira na yau da kullun zuwa tsarin da gwamnati ke goyon baya.

29 Jan, 2026
Gwamnatin Jihar Kano ta tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za ta warware rikicin Masarauta
Waiya ya jaddada cewa gwamnati na daukar matakai na gaske don dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin jihar.

29 Jan, 2026
‘Yansandan Nijeriya sun ƙwato kwamfuta 400, sun kama ɓarayin airtime na Naira biliyan 7.7
Jami’an ‘yansanda a Nijeriya sun kama mutane shida da ake zargi da kutse a kamfanonin sadarwa a Nijeriya da suka yi shirin satar airtime na Naira biliyan 7.7.

28 Jan, 2026
Gwamnatin Jihar Borno ta karɓi ‘yan-gudun-hijirar Nijeriya 300 da suka dawo gida daga Kamaru
‘Yan-gudun-hijirar da suka dawo sun isa garin Pulka ta wata tsararriyar hanya da aka bi, wanda ke nuna wani gagarumin ci gaba da aka samu a ƙoƙarin gwamnatin jihar na sake dawo da ‘yan-gudun-hijira gida na tsawon lokaci.

28 Jan, 2026
Jihar Kwara ta sa dokar hana fita ta awa 24 a yankin Oro-Ago saboda matsalar tsaro
Dokar hana fitan ta fara aiki da karfe 6:00 na safe, a cewar wata sanarwa da shugaban majalisar kananan hukumomi, Femi Yusuf, ya fitar, kuma sakataren yada labaransa, Abdulquadri Jimba ya sanya wa hannu.

28 Jan, 2026
“Ina ma a ce abubuwan da suka faru a siyasar Kano mafarki ne”: Kwankwaso
Jagoran Jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan jihar Kano a Nijeriya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana irin yadda ya ji da ma halin da ya tsinci kansa a ciki bayan da gwamna ɗay na jam’iyyarsu Abba Kabir Yusuf ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.


