11 Sep, 2026

Mutum 511 sun kamu da cutar mashaƙo a Jihar Yobe a Nijeriya

Ya bayyana cewa ɓullar cutar ta shafi ƙananan hukumomi 12 ne a jihar, yana mai ƙarawa da cewa shiri ya yi nisa don ƙaddamar da riga kafi kan cutar a waɗannan yankunan.

173911f9 82e2 4ecf b814 989436839b33 1784728475614

10 Sep, 2026

Amurka ta aika sabbin kayayyakin soji Nijeriya

An kwashe kayan aikin zuwa Nijeriya ne ta jirgin saman sojin Amurka kirar C-17 Globemaster III, ƙarƙashin tsarin sayar da kayan aikin soji na ƙasashen waje tsakanin Washington da Abuja.

673b425c 5c7c 4a65 933a 3e006ee7cd28 1789058121317

10 Sep, 2026

Jakadan Nijeriya ya ziyarci ’yan kasar 198 da ke gidan yari a Indiya

Jakadan Nijeriya a Indiya, Ambasada Saidu Muhammad ya gana da ’yan Nijeriya 198 da ke tsare a lokacin ziyararsa zuwa kurkuku daban-daban a faɗin Indiya.

acf4494e 93a4 4101 b856 ed35ef8e6c7b 1789050356875

10 Sep, 2026

‘Yansandan Nijeriya sun kama mutum biyu kan zargin kashe Danshagamu a Kano

Sanarwar ta ce ana gudanar da bincike kan lamarin kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu da zarar an kammala binciken.

aa2d30e5 f494 4702 9b51 78aa3cd0d4f7 1789025449717

9 Sep, 2026

Nijeriya ta naɗa sabon kwamandan yaƙi da ƙungiyar ta’addanci ta Boko Haram

Nadin Manjo Janar Ibikunle Ademola Ajose na daga cikin sauye-sauyen shugabancin soji da suka shafi wasu janar-janar 14, in ji kakakin rundunar sojin.

b809d7ea ae5f 45f0 b355 9017d5b7f79b 1788970642999 main

9 Sep, 2026

NEMA ta karɓi ’yan Nijeriya 180 da aka mayar da su gida daga Libya

Tawagar ta ƙunshi manya 169 — maza 68 da mata 101 — da kuma yara maza shida, jarirai biyar da kuma mutum ɗaya da ke fama da rashin lafiya.

935a1108 038f 40c5 a967 146a21e75a33 1788960668473

9 Sep, 2026

Sojojin Nijeriya sun kama wasu da ake zargin masu kai wa ’yanta’adda kayayyaki ne a Jihar Yobe

Rundunar ta ce an gudanar da aikin ne ranar Talata, 8 ga Satumba, bayan samun bayanan sirri kan wasu kayayyakin da ake zargin za a wuce da su zuwa ga ’yanta’addan da ke aiki a yankin Yunusari-Mobbar.

b62fe0d0 e949 4569 9805 67635138bd2d 1777388191620

8 Sep, 2026

FIFA ta tura tawaga zuwa Nijeriya don gano ko gwamnati ta tsoma baki a murabus ɗin shugabannin NFF

Wasiƙar ta nuna cewa FIFA ta zartar da wannan mataki ne a taronta na ranar 1 ga Satumba a birnin Zurich, wanda ya haɗa wakilan FIFA, CAF, da NFF, da kuma gwamnatin Nijeriya.

33de2bfe 81e4 414a 95bf 7b2d0625a4a3 1786047435054

8 Sep, 2026

INEC za ta ƙaddamar da na’urar bibiyar shirye-shiryen zaɓe kai-tsaye

Shugaban hukumar, Farfesa Samuel Amupitan ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Legas, yayin wani taron bita na musamman da aka shirya wa Sakatarorin Gudanarwa na hukumar.

258327b3 47ef 4dc4 83ef 9acef9284008 1776674731024

8 Sep, 2026

An kashe mutum 12, an jikkata 2 a sabon harin da aka kai wani ƙauye a Adamawa ta Nijeriya

Harin ya faru ne da safiyar ranar Litinin, kasa da makonni biyu bayan da aka kashe fiye da mutane 10 a wani harin da aka kai a ƙaramar hukumar Hong ta jihar, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

0849398a 8e23 4602 b2b9 123051bcc057 1786463870154
Loading...