Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce tsarin kiwon lafiya a sassan Gabas ta Tsakiya na fuskantar matsin lamba mai tsanani bayan fiye da kwanaki goma da barkewar rikicin da ke ƙara tsananta a yankin. Rahotanni sun nuna cewa dubban mutane sun mutu yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon hare-haren da ke faruwa a ƙasashe daban-daban.
A cewar bayanan da WHO ta tattara, sama da mutane 1,300 sun mutu a Iran yayin da kusan 9,000 suka jikkata. A Lebanon kuma akalla mutane 570 sun mutu tare da jikkata fiye da 1,400, yayin da Isra’ila ta ba da rahoton mutuwar mutane 15 da jikkata 2,142.
Hukumar ta kuma nuna damuwa kan yadda hare-hare ke shafar cibiyoyin kiwon lafiya da ma’aikatansu. Darakta Janar na WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce irin wadannan hare-hare ba kawai suna kashe rayuka ba ne, har ma suna hana mutane samun kulawar lafiya a lokacin da suka fi bukata.
Rikicin ya tilastawa dubban mutane barin gidajensu, inda fiye da 100,000 daga Iran da kuma kusan 700,000 a Lebanon suka rasa matsuguni. WHO ta gargadi cewa rashin ruwa mai tsafta, muhalli mai kyau da kuma ƙarancin kayan jinya na iya ƙara haddasa matsalolin lafiya, musamman ga mata da yara.














