Rukunin ƙarshe na ‘yan sandan ƙasar Kenya sun bar Haiti, wanda hakan ya kawo ƙarshen aikin tsaro na ƙasa da ƙasa (MSS) da aka fara a 2024 domin taimakawa wajen yaƙi da ‘yan bindiga. Duk da ƙoƙarin da aka yi, aikin bai kai ga cikakken nasara ba, musamman a babban birnin Port-au-Prince inda rikicin ya fi tsanani.
Kenya ce ta jagoranci wannan ƙoƙari na ƙasa da ƙasa, inda ta yi alkawarin tura ‘yan sanda 1,000 amma kusan 800 ne kawai aka tura. Haka kuma, aikin ya fuskanci ƙarancin kuɗi, inda aka samu kusan kashi biyu bisa uku na kasafin da aka tsara, lamarin da ya shafi kayan aiki, bayanan sirri da kuma tasirin aikin gaba ɗaya.
Akwai kuma cece-kuce kan zargin wasu jami’ai da aikata ba daidai ba. Duk da cewa an tabbatar da wasu daga cikin waɗannan zarge-zarge tare da taimakawa waɗanda abin ya shafa, hukumomin Kenya sun musanta cewa matsalar ta shafi yawancin jami’an su.
Yanzu wani sabon tsari mai suna Gang Suppression Force zai maye gurbin MSS, inda zai yi aiki kafada da kafada da ‘yan sandan Haiti da sojoji domin dawo da tsaro. Jami’an Haiti sun gode wa Kenya kan taimakon da ta bayar a wani lokaci mai muhimmanci, duk da ƙalubalen da aka fuskanta.
MAJIYAR LABARI: NEWSTIMEHUB














