Ruwan sama mai ƙarfi da aka yi a kudancin ƙasar China ya jawo ambaliyar ruwa kwatsam a yankin Guangxi Zhuang Autonomous Region, lamarin da ya tilasta kwashe mutane daga gidajensu tare da kawo cikas ga rayuwar yau da kullum.
Ambaliyar ta fi tsanani a birnin Qinzhou, inda ruwan ya mamaye wurare tare da toshe hanyoyi, har ma ya sa wasu mazauna suka makale ba tare da hanyar fita ba. Kungiyoyin agaji sun garzaya cikin gaggawa, inda aka tura jami’an kashe gobara da motocin ceto zuwa yankunan da abin ya shafa.
Kimanin mutane 30 da suka makale an samu nasarar ceto su kafin tsakar rana, sakamakon haɗin gwiwar jami’an kashe gobara sama da 150. Hukumomi sun kuma dakatar da karatu a wasu makarantu saboda hatsarin da yanayin ya haifar.
Har yanzu jami’ai na ci gaba da sa ido kan halin da ake ciki, domin irin wadannan guguwar ruwan sama na iya haddasa ambaliya cikin gaggawa, musamman a yankunan da ke da rauni. Babban abin da ake mayar da hankali a kai shi ne kare rayukan jama’a da rage asarar dukiya.
MAJIYAR LABARI: NEWSTIMEHUB












