Wata sanarwa da Benjamin Hundeyin, kakakin rundunar ‘yansandan Nijeriya ya fitar a ranar Laraba, ta ce waɗanda ake zargin sun samu damar yin kutse cikin manyan tsarin kamfanin sadarwa ba bisa ƙa’ida ba.
Waɗanda ake zargin su ne Ahmad Bala, Karibu Mohammed Shehu, Umar Habib, Obinna Ananaba, Ibrahim Shehu, da Masa’ud Sa’ad.
Hundeyin ya ce jami’an sun ƙwace ƙananan wuraren sana’a guda biyu, shagunan sayar da kayayyaki ɗauke da kwamfutocin tafi-da-gidanka fiye da 400, wayoyin hannu 1,000, da kuma wata mota ƙirar Toyota.
Mai magana da yawun rundunar ya ce an gano wani adadi mai yawa na kuɗi a asusun bankin waɗanda ake zargin.
“Ƙungiyar ‘yanta’adda ce ke da alhakin karkatar da airtime na wani kamfanin sadarwa ba bisa ƙa’ida ba, wanda ya haddasa da asarar fiye da Naira biliyan 7.7,” in ji sanarwar.
“Wannan ci gaba ya biyo bayan wani korafi da wani kamfanin sadarwa na Najeriya ya shigar, wanda ya bayar da rahoton ayyukan da ake zargi da kuma wadanda ba a ba su izini ba a cikin tsarin biyan kudi da ayyukan biyan kudi.”
Sanarwar ta kara da cewa bincike ya nuna cewa an yi amfani da bayanan ma’aikatan cikin gida wajen yin kutse, wanda ya bai wa masu barayin damar shiga manyan tsare-tsare ba bisa ka’ida ba.
“Bayan makonni na shiri, an gudanar da ayyukan tsaro cikin tsari a watan Oktoban 2025 a Jihohin Kano da Katsina, tare da kama su a Babban Birnin Tarayya.
Za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala binciken.
“A halin yanzu, Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, Ph.D., NPM, ya yaba wa jami’an da ke da hannu a binciken saboda kwarewarsu.”









