Ƙasashen Afirka sun yi Allah wadai da yadda Isra’ila ta keta alfarmar ‘yancin kan Qatar

Shugaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AUC) ya yi gargaɗin cewa harin na iya barazana ga yanayi mai raunin da ake ciki a gabas Ta Tsakiya.

Newstimehub

Newstimehub

10 Sep, 2025

cdfc4673dc2f546d4de559d6b8e08ed4cbaee768b8104494a09ccefac210885f

Ƙasashen Afirka da Ƙungiyar Tarayyar Afrika sun yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ta kai ranar Talata kan shugabannin Hamas a Qatar, suna masu gargaɗin cewa ta keta ‘yancin kan ƙasar.

Shugaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AUC) ya yi gargaɗin cewa harin zai iya barazana ga yanayi mai rauni da ake ciki a Gabas Ta Tsakiya.

Mahmoud Ali Youssouf ya yi nuni da rawar da Qatar ke takawa a wajen shiga tsakani na diflomasiyya yana mai kira da “a sabunta tattaunawa domin samun zaman lafiya na adalci mai ɗorewa a Gabas Ta Tsakiya”.

Ministan Harkokin Wajen Masar ma ya bayyana harin na Isra’ila a matsayin “tsabar keta dokar ƙasa da ƙasa da kuma ‘yancin kan ƙasa.”

‘Misali mai haɗari’