Turkiyya da Nijeriya sun ƙudiri aniyar kyautata alaƙar kasuwanci, zuba jari da tsaro

Shugaba Erdogan da Shugaba Tinubu sun jagoranci sanya hannu kan yarjeniyoyi tara a yayin da Ankara ke da manufar ƙulla kasuwancin dala biliyan 5 da ƙasa mafi ƙarfin tattalin arziki a Afirka.
28 Jan, 2026
Erdogan da Trump sun tattauna kan Syria da Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza

Shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya faɗa wa Trump cewa yana bin diddigin yarjejeniyar tsagaita wuta da haɗin kai da aka ƙulla ƙarƙashin jogarancin Amurka da gwamnatin Syria.
28 Jan, 2026
Turkiyya ta goyi bayan Nijeriya a yaƙi da ta’addanci yayin da Erdogan ya karbi baƙuncin Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu yana ziyarar aiki ta kwana biyu a Turkiyya26 zuwa 28 ga Janairu.
27 Jan, 2026
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan ya gana da takwaransa na Nijeriya Tuggar

Ministocin biyu sun gana ne a Ankara babban birnin Turkiyya a ranar Litinin.
26 Jan, 2026

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya da takwaransa na Nijeriya za su gana kan cinikayya da tsaro

Turkiyya ta ɗauki dukkan yarjejeniyar zaman lafiyar Gaza da mahimmanci: Erdogan

Fidan na Turkiyya zai halarci bikin sanya hannu na ‘Hukumar Zaman Lafiya’ ta Gaza a Switzerland

An tono makarantar Islamiyya mai shekara 900 yayin aikin sabunta birni a yankin Anatolia a Turkiyya

Filin Jirgin Sama na Istanbul ya zama na biyu mafi hada-hada a Turai a 2025: Erdogan
16 Jan, 2026
Babu wanda ke son sake ɗaukar hoto da Netanyahu, in ji Ministan Harkokin Wajen Turkiyya
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya ya ce manufofin Netanyahu, da suka janyo mutuwa da rushe gine-gine a yankin, sun mayar da Isra’ila saniyar ware.

13 Jan, 2026
Turkiyya ta yi gargaɗi kan tsoma baki daga waje a Iran, ta buƙaci a magance rikicin a cikin gida
Kakakin Jam’iyyar AK mai mulki a Turkiyya Omer Celik ya jaddada cewa tsoma baki, musamman wanda Isra’ila take rura wutarsa, na iya jawo babban rikici da rashin zaman lafiya mai zurfi a Gabas ta Tsakiya.

9 Jan, 2026
Turkiyya na sanya ido sosai kan rikici a Syria a wani bangare mai muhimmanci kan tsaron kasarta
Majiyoyin tsaron Turkiyya sun shaida wa TRT World cewa Turkiyya tana bibiyar rikicin da ake yi a Syria don kare fararen hula da hana kwararar ‘yan gudun hijira saboda yaƙin da ake yi a Aleppo tsakanin sojojin Syria da ƙungiyar ta’addanci ta YPG.

5 Jan, 2026
Erdogan ya yi kira da a dawo da Turkiyya ga shirin samar da F-35 da Amurka ke jagoranta
Karbar jiragen F-35 da Turkiyya ta yi wanda ta riga ta biya da kuma mayar da ita cikin shirin na da muhimmanci kuma ya zama dole do karfafa alaka da Amurka da NATO, Erdogan ya fada wa Bloomberg.

1 Jan, 2026
Dubban mutane sun yi gangami a Istanbul na goyon bayan Falasɗinawa
Gangamin wanda shugabannin addini da na ƙungiyoyin kare hakkin ɗan’adam suka jagoranta mai taken “Ba Za Mu Yi Shiru ba”, wato “We Do Not Remain Silent” a Turancin Ingilishi, ya samu halartar ƙungiyoyi fiye da 400.

31 Dec, 2025
Turkiyya ta fara gina tashar sararin samaniya a Somalia: Minista
Tashar za ta yi aiki da fannin sararin samaniya na duniya, don kawo wa Turkiyya kudin shiga, yayin da za ta taimaka wajen habakar tattalin arzikin Somaliya, in ji Ministan Kasuwanci da Fasaha Mehmet Fatih Kacir.

24 Dec, 2025
Shugaban Turkiyya ya yi wa Firaiministan Libya ta’aziyya kan mutuwar babban hafsan sojin ƙasar
Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya yi ta’aziyya ga Abdul Hamid Dbeibah ta wayar tarho bayan hatsarin jirgin sama a Ankara da ya kashe babban hafsan sojojin Libya, in ji daraktan sadarwa na Turkiyya.

23 Dec, 2025
Turkiyya ta soki ta’addancin RSF a Sudan, ta yi kiran gaggawa don bayar da damar ayyukan jinƙai
Jakadan Turkiyya a Majalisar Ɗinkin Duniya Ahmet Yildiz ya ce Sudan ta zama waje mafi girma a duniya da ke fuskantar rikicin tsugunar da jama’a, inda ya ƙara da cewa “Halacci da tattaunawa” ne kaɗai za su kawo mafita.

20 Dec, 2025
Turkiyya ta kai rukunin farko na tantuna 30,000 da za ta kai Sudan a matsayin agaji
Jirgin kayan ya isa Port of Sudan inda aka tarbe shi ta hannun Mataimakin Shugaban Hukumar Kula da Bala’o’i da Ayyukan Gaggawa ta Turkiyya (AFAD), Hamza Taşdelen, da jakadan Turkiyya a Sudan, Fatih Yıldız.

16 Dec, 2025
Shirin kawar da shara na Matar Shugaban Turkiyya ya tsara taswirar Ankara na karbar bakuncin COP31
Yayin da Turkiyya ta shirya karɓar bakuncin babban taron sauyin yanayi na duniya na 2026, gagarumin shirin Matar Shugaban Ƙasar ya tashi daga matakin fafutuka zuwa ga tsarin kula da yanayi na duniya.

