Shugaban Erdogan ya jinjina wa shekara 25 na Jam’iyyar AK kan samar da ‘sauyi mai tarihi’ a Turkiyya

Yayin da jam’iyyar AK ta cika shekaru 25, Erdogan ya ce an kafa ta ne a ranar 14 ga Agustan 2001, da nufin sake fasalin makomar Turkiyya, ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin gwamnati da ’yan ƙasa, da tabbatar da cewa ƙasar za ta iya yanke shawara da kanta.

Newstimehub

Newstimehub

14 Aug, 2026

1e0ccfe4 8027 4d1e 842c 8d5670a9434b 1786700784637

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce tafiyar shekaru 25 da Jam’iyyar Adalci da Ci Gaba (AK Party) ta yi ta kawo “sauyi mai tarihi” a Turkiyya, yana mai jaddada nasarorin jam’iyyar a fannonin dimokuraɗiyya, ababen more rayuwa, tsaro, fasaha da manufofin ƙasashen waje.

A cikin wata ƙasida da ya rubuta domin bikin cikar jam’iyyar shekaru 25, Erdogan ya ce an kafa AK Party ne a ranar 14 ga Agustan 2001, da nufin sake fasalin makomar Turkiyya, ƙarfafa alaƙar da ke tsakanin gwamnati da ’yan ƙasa, da kuma tabbatar da cewa ƙasar za ta iya yanke shawara da kanta.

“Babu wani abu da zai sake kasancewa kamar yadda yake a Turkiyya,” kamar yadda Erdogan ya maimaita a irin kalaman da ya yi a lokacin da aka kafa jam’iyyar inda ya ƙara da cewa babban abin da ke ba jam’iyyar ƙwarin gwiwa shi ne ra’ayin jama’a.

Ya ce jam’iyyar ta zama “abar da kowa ke fata” ga miliyoyin mutane da suka fuskanci takunkumi kan ’yancinsu, suka ɗauki nauyin matsalolin ƙasar kuma suke neman makoma mafi wadata ga ’ya’yansu.

“Idan muka waiwaya a yau, za mu ga cewa ɗaya bisa huɗu na ƙarni da AK Party ta yi ya yi daidai da wani sauyi mai tarihi ga Turkiyya,” kamar yadda Erdogan ya bayyana.

Ya ce an ƙarfafa halaccin dimokuraɗiyya, an inganta ikon gwamnati na samar da ayyukan jama’a, sannan an faɗaɗa damar mutane ta shiga harkokin gwamnati da rayuwar al’umma.

Da yake magana kan yunƙurin juyin mulkin 15 ga Yulin 2016, wanda ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin “manyan gwaje-gwajen” halaccin dimokuraɗiyya, Erdogan ya ce al’ummar Turkiyya sun nuna cewa babu wani ƙarfi da ke wajen akwatin zaɓe da za ta iya yanke makomar ƙasar.

Ya ce wannan matsaya ta zama wani juyi mai tarihi wajen kawo ƙarshen zamanin katsalandan, ƙarfafa siyasar farar-hula da kuma inganta dimokuraɗiyyar ƙasar.

Zuba jari, masana’antar tsaro da siyasa

Erdogan ya jaddada irin zuba jarin da aka yi a fannonin ilimi, kiwon lafiya, sufuri, makamashi, manufofin jin daɗin jama’a da bunƙasa birane, yana mai cewa an faɗaɗa ayyukan gwamnati a faɗin ƙasar tare da ƙarfafa shiga harkokin tattalin arziki da zamantakewa.

Ya kuma yi nuni da ci gaban da aka samu a masana’antar tsaro da fasahar zamani, yana cewa Turkiyya ta rage dogaro da masu samar da kayayyaki daga ƙasashen waje a wasu muhimman fannoni.

Ya ambaci jiragen sama marasa matuƙa, jirgin yaƙin KAAN da aka ƙera a cikin gida, jiragen ruwan yaƙi da tsarin kare sararin samaniya, da kuma motar lantarki ta TOGG, shirin sararin samaniyar ƙasar, zuba jari a makamashin nukiliya da kuma gano iskar gas a Tekun Bahar Maliya, a matsayin alamomin “sabon kwarin gwiwar” Turkiyya.

“A nan gaba, za mu mayar da wannan ƙwarewar da muka tara zuwa wani sabon ci gaba a fannonin fasahar basirar wucin gadi, semiconductor, fasahar makamashi da samar da kayayyaki masu daraja mai yawa.”

“Duniya ta fi ƙasashe biyar girma”

Erdogan ya ce Turkiyya ta zama ƙasa mai tasiri a tsarin duniya da ke ƙara samun ƙasashe masu ƙarfin iko da dama, tana bin manufofin ƙasashen waje masu fuskoki da dama bisa la’akari da muradun ƙasa, diflomasiyya, tattaunawa da kuma nauyin jinƙai.

Ya ce Turkiyya ta ƙarfafa alaƙarta da ƙasashen Turkawa da Musulmi, tare da kare haƙƙin waɗanda ake zalunta a dandalin ƙasa da ƙasa.

Ya bayyana Turkiyya a matsayin ƙawa mai ƙarfi ta NATO, mamba mai taka rawa a G20, ɗaya daga cikin manyan mambobin Ƙungiyar Haɗin Kan Musulunci (OIC), da kuma muhimmiyar ƙasa a tsarin tsaron Turai.

“Daga Tekun Bahar Maliya zuwa Gabas ta Tsakiya, daga Caucasus zuwa Afirka, muna bayar da gudunmawa wajen zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin wani yanki mai girma,” in ji shi.

Erdogan ya kuma sake nanata kiransa kan cewa “duniya ta fi ƙasashe biyar girma,” yana mai neman a ƙara wakilci da a cibiyoyin ƙasa da ƙasa, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya.

Kalubale da farfaɗo da yankunan da girgizar ƙasa ta shafa

Erdogan ya ce jam’iyyar ta fuskanci ƙalubale da dama cikin tafiyarta ta shekaru 25, ciki har da hare-haren ta’addanci, yaƙe-yaƙen yankuna, ƙaura ba bisa ƙa’ida ba, annobar COVID-19 da kuma sauye-sauyen tattalin arziki.

Da yake magana kan girgizar ƙasa ta 6 ga Fabrairu, 2023, ya ce bala’in ya shafi larduna 11 da miliyoyin ’yan ƙasa, tare da haifar da “manyan raunuka” a faɗin ƙasar.

Ya ce gwamnati ta tattara dukkan albarkatun ƙasa tun daga farkon bala’in, kuma ta samu gagarumin ci gaba wajen sake gina biranen da girgizar ƙasar ta shafa, ciki har da gidaje, kayayyakin haɗa abubuwa, ababen more rayuwa, ayyukan jin daɗin jama’a da kuma kare wuraren tarihi.

“Sabunta kanmu alhakinmu ne”

Erdogan ya ce ƙarfin AK Party cikin shekaru 25 ya samo asali ne daga “ƙulla alaka ta zukata” da al’ummar Turkiyya, amma ya ƙara da cewa wannan tarihi ya zo da alhakin ci gaba da sabunta jam’iyyar.

Ya ce dole jam’iyyar ta yi nazari a fili kan sauye-sauyen buƙatun jama’a, neman makoma da matasa ke yi, tasirin matsalolin tattalin arziki kan rayuwar yau da kullum da kuma yadda siyasa ke gudana a ƙasar.

Ya yi alƙawarin ci gaba da yaƙi da hauhawar farashin kayayyaki tare da faɗaɗa samar da kayayyaki, zuba jari da samar da ayyukan yi.

Ya ce: “Za mu yi aiki domin Turkiyya wadda ake ba masu aiki tuƙuru ladan aikinsu, wadata ta yaɗu ga dukkan sassan al’umma, sannan matasanmu su samu damar yin karatu, samun aikin yi, kafa sana’o’i da samun gidaje cikin adalci.”

Ya bayyana “Century of Türkiye” (Ƙarnin Turkiyya) a matsayin hangen nesa na bai ɗaya na ƙasar na ƙarni na biyu na Jamhuriyar Turkiyya.

Ya ce: “Ƙarnin Turkiyya shi ne sunan ƙudurinmu na bai ɗaya na makomar ƙarni na biyu na Jamhuriyarmu. Muna hangen Turkiyya mai ƙarfi wajen dimokuraɗiyya, tattalin arziki mai samar da kayayyaki, jagoranci a fasaha, manufofin ƙasashen waje masu tasiri da kuma ƙaƙƙarfan haɗin kan jama’a.”

Erdogan ya ce cikar AK Party shekaru 25 “wani muhimmin mataki ne na tarihi” da ke ba jam’iyyar damar duba irin ƙwarewar da aka samu a baya tare da tsara taswirar hanyar sabon zamani.

Ya ƙara da cewa jam’iyyar za ta ci gaba da tafiyarta da irin wannan ƙuduri, ta hanyar ci gaba da aiwatar da manufofinta na sauyi da kuma mayar da hankali kan damammakin da gaba za ta samarwa.