An ji ƙarar harbe-harben bindigogi da dama a safiyar Alhamis ɗin nan a filin jirgin sama na Yamai, babban birnin Jamhuriyar Nijar, kamar yadda mazauna yankin suka shaida wa kamfanin dillacin labarai na AFP, watanni da dama bayan wani babban hari da aka kai filin jirgin.
“Na ji ƙarar bindiga ta farko da misalin ƙarfe 6 na safe (0500 GMT). Karar harbin na fitowa ne daga hanyar shiga filin jirgin saman, kuma ƙarar harbin ya ci gaba har tsawon sa’o’i biyu bayan haka,” in ji wani mazaunin yankin da ya zanta da AFP ta wayar tarho.
Shi ma wani mazaunin yankin ya tabbatar da cewa harbe-harben na faruwa ne a daidai ƙofar shiga filin jirgin saman.
A watan Janairun da ya gabata, an kai wa Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Diori Hamani da ke babban birnin ƙasar wani mummunan hari na ba-zata, wanda ƙungiyar ta’addanci ta EIS ta ɗauki alhakin kaiwa, inda dakarun tsaron Nijar da mayaƙan Rasha da ke ƙawance da su suka fatattaki maharan.
Kafin faruwar hakan, tashe-tashen hankula na ‘yan ta’adda a ƙasar Nijar sun taƙaita ne kawai a wasu sassan ƙasar.
Biyo bayan harin na watan Janairu, hukumomi sun rusa dubban gidajen da aka gina ba bisa ƙa’ida ba a wata unguwa da ke kusa da filin jirgin saman.
Hukumomi sun bayyana cewa ‘yan ta’adda sun mamaye unguwar, inda suka saje da mazaunanta domin ƙaddamar da harin.
Nijar, ƙasa mai faɗin gaske a yankin Sahel na yammacin Afirka, ta kwashe tsawon shekaru goma tana fama da tashe-tashen hankula daga ƙungiyoyin ta’addanci.















