Sojojin Sudan sun ƙwace ƙauyen Al-Kurmuk bayan arangama da dama da RSF

Al-Kurmuk yana da muhimmanci sosai wajen sarrafa hanyoyin safarar kayayyakin soji da hanyoyin da suka haɗa Ethiopia ko Habasha da Sudan ta Kudu.

Newstimehub

Newstimehub

8 Jul, 2026

5eac08198a8ad4bd4f0f5c20527ac26c7c7baa0f657d5bd7c8721f97559d8b00

Dakarun sojin Sudan sun shiga garin Al-Kurmuk mai muhimmanci a gabashin Sudan a ranar Laraba bayan fafatawa da dama da dakarun sa-kai ta RSF, in ji majiyoyin soja ga Anadolu.

Majiyoyin, waɗanda suka yi magana bisa sharaɗin a ɓoye sunayensu, sun ce dakarun soja da ƙungiyoyin haɗin gwiwa sun shiga Al-Kurmuk bayan jerin ayyukan soja kan ‘yan RSF da SPLM-N, inda suka sake kwace iko da garin.

Matakin ya biyo bayan nasarorin da sojin Sudan suka samu kwanan nan a jihar Blue Nile, inda suka sake ƙwato wurare da dama kusa da iyakokin Ethiopia da Kudancin Sudan, in ji majiyoyin.

Al-Kurmuk na ɗaya daga cikin manyan garuruwa a jihar Blue Nile, tare da birnin jihar, Ad-Damazin. Yana kusa da iyakar Habasha, kuma yana da muhimmanci ta fuskar dabaru saboda ta nan ne ake safarar kayan soji da hanyoyin mota da ke haɗa Sudan da Habasha da Kudancin Sudan.

A ranar 24 ga Maris ne RSF ta kwace iko da Al-Kurmuk.

Sudan ta kasance cikin rikici tun Afrilun 2023, lokacin da yaƙi ya ɓarke tsakanin soja da RSF kan shirin shigar da rundunar RSF cikin rundunar sojin ƙasa.

Rikicin ya haifar da ɗaya daga cikin mafi munin rikice-rikicen jinƙai a duniya, inda ya janyo asarar dubban rayuka kuma ya tilasta wa kusan mutane miliyan 13 barin gidajensu.