Gwamnatin Ethiopia ta sanar da kwanaki uku na makokin ƙasa bayan zaftarewar ƙasa a kudancin ƙasar da ta yi sanadin mutuwar akalla mutane 80. Kakakin Majalisar Wakilai ta Jama’a, Tagesse Chafo, ya ce makokin za su fara ne daga ranar Asabar bayan mummunar iftila’in da ya faru a yankin Gamo.
An ce zaftarewar ƙasar ta faru ne sakamakon ruwan sama mai ƙarfi da ya janyo rushewar ƙasa a yankunan zama tun ranar Talata. Mutane da dama sun rasa rayukansu yayin da wasu da yawa har yanzu ba a gano su ba. Ƙungiyoyin ceto na ci gaba da neman waɗanda suka makale ko suka ɓace, amma ruwan sama da ke ci gaba da sauka na hana aikin tafiya yadda ya kamata.
Jami’in sadarwa na yankin, Hailemariam Tesfaye, ya ce an ƙara ƙaimi wajen ayyukan bincike da ceto domin gano sauran mutane. A cewar Ethiopian Human Rights Commission, akalla mutane 3,461 sun rasa matsugunansu sakamakon wannan bala’i, kuma gwamnati na haɗa kai da hukumomin yankuna domin tallafa wa waɗanda abin ya shafa.
Lamarin ya zo ne a lokacin da ruwan sama na kakar damina ke haddasa matsaloli a sassa da dama na Gabashin Afirka. A makwabciyar Kenya, ambaliyar ruwa ta riga ta yi sanadin mutuwar mutane da dama, yayin da masana daga IGAD Climate Prediction and Applications Centre ke gargadin cewa daminar Maris zuwa Mayu na iya kawo ruwan sama fiye da yadda aka saba a yankin.














