Yaƙin da ake yi da ta’addancin Daesh yana ƙara ƙarfi: Erdogan

Shugaban Turkiyya ya ce kawar da ta’addancin ‘yan a-aware da ke barazana ga arewacin Syria zai kawo sauƙi ga ɗaukacin yankin.

Newstimehub

Newstimehub

25 Jan, 2026

c80de4d6abc3a4cd727181e6ae1c2240af3739fbe57c8563d42bd3f71af8f90f

Yaƙin da ake yi da ƙungiyar ta’addanci ta Daesh yana ƙara ƙarfi da karsashi, inda ake tumɓuke ainihin rushin ta’addanci daga yankin Gabas ta Tsakiya, a cewar shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan.

“Da zarar an kawar da barazanar ta’addanci ta ‘yan a-aware daga arewacin Syria, ba al’ummar Syria ne kawai za su samu sauƙi ba, har da sauran al’ummar yankin,” in ji Erdogan a ranar Asabar a wajen bikin miƙa sabbin gidaje da aka gina a lardin Aydin na ƙasar Turkiyya.

Ya jaddada buƙatar haɗa kai da tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a Syria yana mai cewa hakan zai amfani dukkan al’ummominta.

Ya ƙara da cewa, “waɗanda za su ci moriya idan aka haɗa kai da samar da zaman lafiya a Syria su ne Larabawa, Turkmaniyawa, Kurdawa, Alawiyawa, Druze, Kiristoci da dukkan al’ummar Syria.”.

Da yake magana kan harkokin duniya, Erdogan ya ce muhawarar da ake yi a wannan makon a wurin taron tattalin arzikin duniya na World Economic Forum a birnin Davos ya nuna cewa ƙasashen yammacin duniya suna goyon bayan daɗaɗɗen matsayin Turkiyya na sukar tsarin duniya na yanzu.