Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP, sun lalata motocin ƙunar-baƙin-wake na ‘yan ta’adda

‘Yan ta’addan sun yi yunkurin kutsawa cikin sansanin soji na Mairari ta hanyar amfani da motocin ƙunar-baƙin-wake guda biyu. Sai dai sojojin da ke aikin sa ido sun gano tare da tarwatsa motocin kafin su kai ga shiga sansanin.
14 Dec, 2025
Shugaba Tinubu ya amince da kafa sabuwar makarantar horar da kuratan sojoji a Abakaliki

Shugaban Sojin Ƙasa na Nijeriya Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya ce ana sa ran sabon depot ɗin da za a buɗe a Abakaliki zai fara aiki nan gaba kaɗan sannan kuma ya tallafa wa sauran wuraren horar da kuratan soji da ke Zaria da Osogbo.
13 Dec, 2025
Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda ta tabbatar da hukuncin kisa

A watan Oktoba ne Shugaba Tinubu ya yi wa Maryam afuwa ta hanyar sassauta mata hukuncin daga na kisa zuwa na zaman gida yari na shekaru 12 a bisa dalilai na tausayawa.
12 Dec, 2025
Aƙalla sojojin Nijeriya da Ivory Coast 200 sun isa Benin bayan an daƙile yunƙurin juyin mulki

Yunƙurin juyin mulkin ya girgiza Benin ranar Lahadi, lamarin da ya sa Nijeriya da Ivory Coast suka tattara dakaru domin tallafa wa gwamnatin na farar-hula.
12 Dec, 2025

Majalisar Wakilan Nijeriya ta nemi gwamnati ta bayar da rangwamen haraji ga kamfanonin jiragen sama

Saɓanin da ya kunno kai tsakanin Majalisar Dattijan Nijeriya da Shugaba Tinubu kan janye ‘yansanda

Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kashe ɓarayin daji 11 a Sokoto

Remi Tinubu ta yi watsi da zargin tsayar da gwamnan Osun daga yin waka a taron nadin sarautarta

Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tura sojoji Jamhuriyar Benin
9 Dec, 2025
Rundunar sojin saman Nijeriya ta musanta keta sararin samaniyar Burkina Faso
Rundunar sojin saman Nijeriya ta ce jami’anta suna cikin aminci kuma sun sami tarba mai kyau a Burkina Faso, sai dai kuma ƙungiyar AES ta ce duk wani jirgin da ya keta alfarmar sararin samaniyarta za a yi kaca-kaca da shi.

9 Dec, 2025
Gwamnatin Jihar Neja ta karɓi ɗalibai 100 na St. Mary’s Catholic School da aka ceto
Ɗaliban na makarantar St. Mary’s Catholic School sun isa gidan gwamnatin Jihar Neja ne a cikin motocin bas da misalin ƙarfe 5:20 na yamma sannan Gwamna Bago da wasu jami’an gwamnatinsa suka tarbe su.

8 Dec, 2025
Kotu ta yi watsi da buƙatar Nnamdi Kanu ta a ɗauke shi daga gidan gyaran yari na Sokoto
Mai shari’a James Omotosho na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ya ƙi amincewa da buƙatar Nnamdi Kanu, jagoran ƙungiyar IPOB, ta a ɗauke shi daga gidan gyaran hali na Sokoto uzwa Abuja ko kuma Jihar Nasarawa mai maƙwabtaka.

8 Dec, 2025
Shugaba Tinubu ya jinjina wa sojojin Nijeriya kan daƙile juyin mulki a Benin
Bayan buƙatar da gwamnatin Benin ta yi sau biyu, Shugaba Bola Tinubu ya umarci jiragen yaƙin Nijeriya su shiga ƙasar inda suka ƙwace ikon sararin samaniyarta domin daƙile masu iƙirarin juyin mulkin da ke gidan talbijin na ƙasar da wani sansanin soji.

8 Dec, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta karɓo ɗalibai 100 da aka sace daga St. Mary’s Catholic School a Jihar Neja
‘Yanbindiga sun kai hari a makarantar St. Mary’s Catholic School da ke Papiri a Jihar Neja ne ranar 21 ga watan Nuwamba inda suka sace mutum 315 — ɗalibai 303 da malamai 12.

7 Dec, 2025
Tawagar Majalisar Dokokin Amurka ta isa Nijeriya, ta tattauna da Nuhu Ribadu
Babban Mai Bai wa Shugaban Nijeriya Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu ya ce tawagar ta je Nijeriya ne domin tattara bayanai bayan tattaunawar diflomasiyya da tawagar Nijeriya ta yi a Washington a kwanakin baya kan zargin tauye haƙƙin addini.

6 Dec, 2025
Gwamnatin Nijeriya za ta fara rufe wuraren sana’ar POS marasa rajista daga Janairun 2026
Hukumar da ke yi wa Kamfanonin Rajista a Nijeriya ta yi gargaɗi game da masu gudanar da sana’ar POS ba tare da rajista ba inda ta ce daga Janairun 2026, jami’an tsaro za su fara rufe duk wani wurin sana’ar POS maras rajista.

5 Dec, 2025
Kakakin Majalisar Jihar Ribas da wasu ‘yan majalisa 16 sun sauya sheƙa daga PDP zuwa APC
Majalisar ta gudanar da zamanta a yau, inda waɗanda suka sauya sheƙar suke cewa sun bar jam’iyyar ta PDP ne saboda rikicin cikin gida da ya addabi jam’iyyar.

5 Dec, 2025
Ghana na shirin kashe dala biliyan 3.4 a fannin makamashin da ake iya sabuntawa
Ministan makamashin ƙasar Ghana John Abdulai Jinapor ne ya bayyana wannan shirin ranar Laraba a taron makamashin da ake sabuntawa na Afirka (REFA 2025) da aka yi a birnin Accra.

4 Dec, 2025
Majalisar Tattalin Arzikin Nijeriya ta amince da N100bn don gyara cibiyoyin horas da ‘yansanda
An ɗauki wannan matakin ne a taron majalisar na 154 inda majalisar ta amince domin gyara cibiyoyin horas da ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro a faɗin ƙasar.


