An kashe fiye da mutum 30, an sace wasu da dama a Jihar Niger a tsakiyar Nijeriya: ‘yansanda

Mahara sun kashe fiye da mutum 30 sun kuma sace wasu da dama a jihar Neja ta arewa ta tsakiyar Nijeriya, kamar yadda ‘yansanda suka bayyyana a ranar Lahadi.
4 Jan, 2026
Sojojin Nijeirya sun gano albarusai masu yawa a cikin kwata a Maiduguri

Hukumomi sun ce tuni aka dauki matakin tabbatar da cewa lamarin bai jefe rayuwar jama’a cikin hadari ba, yayin da ake ci gaba da yunƙurin kwashe ruwan da ke cikin kwatar ko za a gano wasu karin makaman.
3 Jan, 2026
Eric Chelle: An zaɓi kocin Nijeriya a matsayin gwarzon koci a zagayen rukuni na AFCON 2025

Daga tawagar Super Eagles ta Nijeriya, Ademola Lookman aka zaɓa a matsayin ɗanwasan tsakiya mai kai hari daga gefen hagu. Lookman ya ci ƙwallo 2 a wasanni 3 da ya buga zuwa yanzu.
2 Jan, 2026
Sakon Shugaba Tinubu na sabuwar shekara: Za a tallafa wa mutum 1,000 a kowace mazaɓa a Nijeriya

Shugaban na Nijeriya ya kuma bayyana cewa za a haɓaka tattalin arzikin ‘yan ƙasar ta hanyar bunƙasa harkokin noma, da cinikayya da sarrafa abinci da hakar ma’adinai.
1 Jan, 2026

An sallami Anthony Joshua daga asibiti

Rundunar sojin Nijeriya ta kashe ‘yan ta’adda 47 a farmaki da ta kai a faɗin ƙasar

Gobara ta ƙona Masallacin Shitta-Bey mai tarihi a Lagos wanda ke da alaƙa da Daular Turkiyya

Kotu ta ba da umarnin tsare Abubakar Malami da ɗansa a gidan yarin Kuje

Wani abu ya fashe a Babban Asibiti a Jihar Kebbi ta Nijeriya
30 Dec, 2025
‘Yan jarida bakwai sun mutu sakamakon hatsarin mota a Gombe
Tayar motar bas din da suke cikince ta fashe a hanyarsu ta dawo wa.

29 Dec, 2025
Siyasar Kano: Shin Kwankwaso ne zai tura Gwamna Abba Jam’iyyar APC ko kuwa gaban kansa yake son yi?
A siyasar Nijeriya ba sabon abu ne sauya shekar masu mulki daga jam’iyyun da suka yi nasara a karkashinsu zuwa wasu jam’iyyun na daban, inda a baya bayan nan wasu gwamnonin jam’iyyun adawa suka koma jam’iyyar APC mai mulkin Nijeriya.

28 Dec, 2025
Shugaba Tinubu ya tafi Turai don ci gaba da hutun ƙarshen shekara
Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Nijeriya, Bayo Onanuga, ya wallafa a shafinsa na X, ba ta faɗi ƙasar da Shugaba Tinubu zai je a Turai ba, da ma kwanakin da zai kwashe a can.

28 Dec, 2025
Bam da aka binne a titi ya hallaka mutane Jihar Zamfara, wasu da dama sun jikkata
Runduanr ‘yansandan jihar ta tabbatar da fashewar bam ɗin a ranar Asabar da rana, sai dai ba ta yi ƙarin bayani kan yawan waɗanda suka mutu da waɗanda suka jikkata ba. Amma kafofin watsa labaran kasar suna rawaito cewa aƙalla mutum 7 ne suka mutu.

27 Dec, 2025
Mun tunkari Turkiyya domin neman agaji kan matsalar tsaro – Shugaban Nijeriya Tinubu
Tinubu ya kuma ce gwamnatinsa ba ta yin ƙasa a gwiwa a ƙoƙarinta ta dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ƙasar, “duk da dabarun yakin sunƙuru da ‘yanbindiga suke yi,” in ji shi.

27 Dec, 2025
Hare-haren Amurka sun sauka a wuraren da babu ‘yan ƙungiyar Daesh a Sokoto, in ji mazauna yankin
Wani ɗan majalisar dokoki ya bayyana ƙauyen Jabo a matsayin wurin da ake da ‘zaman lafiya’ wanda ba shi da wani tarihi ‘na kasancewar ‘yan ƙungiyar Daesh, ko Lakurawa, ko ma duk wata ƙungiyar ta’addanci.’

27 Dec, 2025
Jirgin Saman Sojin Nijeriya C-130 da aka tsare a Burkina Faso ya isa Portugal domin yin gyara
An kwashe makonni ana taƙaddamar diflomasiyya tsakanin ƙungiyar AES da Nijeriya bayan saukar gaggawa da jirgin saman kirar C-130 ya yi a Burkina Faso sakamakon matsalar na’ura.

26 Dec, 2025
Da haɗin gwiwarmu Amurka ta kai hari Nijeriya: Ma’aikatar Harkokin Waje
Da tsakar daren Alhamis ɗin nan ne a wani saƙo ta shafin sada zumunta na Truth Social, Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar cewa Ma’aikatar Yaƙi ta ƙasarsa ta kai hare-hare a kan ‘yan ta’adda na ƙungiyar ISIS (Daesh) a arewa maso yammacin Nijeriya.

26 Dec, 2025
Amurka ta kai hari kan mayaƙan Daesh a Nijeriya, in ji Donal Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Ma’aikatar Yaƙi ta ƙasarsa ta kai hare-haren a kan ‘yan ta’adda na ƙungiyar ISIS (Daesh) da ke arewa maso yammacin Nijeriya.

25 Dec, 2025
Gobara ta lalata katafaren ginin GNI mai hawa 22 da wasu da ke jikinsa a Lagos
Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu ya yi magana game da lamarin, yana mai kira ga mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da tabbatar musu da cewa an shawo kan gobarar.


