Dan wasan gaba na Liverpool, Mohamed Salah, ya soki martanin UEFA dangane da mutuwar Suleiman Al-Obeid, wanda aka fi sani da “Pele na Falasdinawa,” bayan hukumar kwallon kafa ta Turai ta kasa bayyana cewa an kashe shi ne ta hanyar harin Isra’ila yayin da yake jiran abinci na agajin jinkai a Gaza da aka yi wa ƙawanya.
A cikin wani gajeren rubutu a shafin sada zumunta na X a ranar Asabar, UEFA ta bayyana tsohon dan wasan ƙungiyar ƙasar Falasɗinu a matsayin “wani mai baiwa da ya ƙarfafa gwiwowin yara marasa adadi, har a cikin lokuta mafi muni.”
Sai dai, sakon UEFA bai bayyana yadda ya mutu ba, kuma babu wani kalami na Allah wadai ko kira ga tsagaita wuta.
Salah ya mayar da martani ga sakon da cewa: “Za ku iya fada mana yadda ya mutu, a ina, kuma me ya sa?”
Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta Falasdinu ta bayyana cewa Al-Obeid, mai shekaru 41, ya mutu ne sakamakon harin da Isra’ila ta kai kan fararen hula da ke jiran tallafin jin kai a kudancin Gaza.
Salah, wanda ke daya daga cikin manyan taurarin gasar Premier League, mai shekaru 33 wanda asalin ɗan Masar ne, ya taba yin kira a baya don a ba da damar kai tallafin jin kai zuwa Gaza tare da kira ga tsagaita wuta.