Majalisar Dokokin Turkiyya ta yi kira kan a dakatar da Isra’ila daga MDD kan kisan ƙare-dangi a Gaza

Israila ta kashe kusan Falasɗinawa 63,000 a Gaza tun daga Oktoban 2023. Yaƙin ya lalata yankin wanda a halin yanzu yake fuskantar yunwa.

Newstimehub

Newstimehub

30 Aug, 2025

1b25daf1541bb1f207d2b3ba246d20028a2e138839e2e871b46fe1d1dffc9907

Majalisar Dokokin Turkiyya ta amince da wani kudiri mai tsauri da ke yin Allah wadai da Isra’ila kan faɗaɗa mamayar da take yi wa Gaza da kuma kisan kare-dangin da take yi wa Falasɗinawa.

A cikin sanarwar da ta fitar, majalisar ta bayyana cewa: “Muna kira da a dakatar da Isra’ila daga kasancewa mamba a Majalisar Dinkin Duniya da sauran ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa har sai ta dakatar da manufofinta na kisan kare dangi.”

Kudirin ya kuma yi kira ga dukkan majalisun dokoki na kasa da su yanke duk wata alaka ta soja da kasuwanci da Isra’ila, tare da daukar matakan cire takunkumin da aka kakaba wa Falasdinu.

Sanarwar ta fito ne a karshen wani zama na musamman da mjalisar ta yi kan halin da ake ciki a Gaza.

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya yi jawabi a zaman, inda ya yi wa ‘yan majalisar bayani kan matsalar jin kai da ake fuskanta a Gaza.