Isra’ila ta kai hari kan shugabannin Hamas da suka taru a Qatar don tattaunawa kan tsagaita wuta

Qatar ta yi Allah-wadai da abin da ta kira harin matsorata da Isra’ila ta kai kan kasarta.

Newstimehub

Newstimehub

9 Sep, 2025

bf350c9d0c4a3fe0f3736bca7d6c1387387ae396d821d3ad85f3545f4d30bf20

Kamfanin dillancin labaran Reuters ya bayar da rahoton cewa, Isra’ila ta tabbatar da cewa ta kai wani hari kan manyan shugabannin kungiyar Hamas, ko da yake ba ta bayyana inda aka kai harin ba.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da kafafen yada labarai daga Qatar suka ce an ji ƙarar fashewar wasu abubuwa a Doha babban birnin kasar, tare da turnuƙin hayaƙi da ke tashi sama.

Wani babban jami’in gwamnatin kasar Isra’ila ya shaida wa kafofin yada labaran kasar cewa harin ya rutsa da mataimakin shugaban kungiyar Hamas Khalil al-Hayya da kuma babban jami’in kasar Zaher Jabareen.

Wata tawagar shugabannin Hamas ta tsallake rijiya da baya a harin na Doha, kamar yadda wani babban shugaban kungiyar ya shaida wa Al Jazeera.

Jami’an Isra’ila sun kuma shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa an kai harin ne kan shugabannin Hamas a Qatar, sai dai ba a sami karin bayani kan asarar rayuka ko kuma girman harin ba.