Iran ta kama mutane 500 kan zargin leƙen asiri

Hukumomin Iran sun sanar da kama mutum 500 bisa zargin leƙen asiri tun bayan da Amurka da Isra’ila suka fara kai hare-hare kan ƙasar. Babban hafsan ‘yansandan ƙasar ya ce an kama mutanen ne saboda zargin ba da bayanai ga abokan gaba da kuma kafafen watsa labarai masu hamayya. A cewarsa, akalla mutum 250 daga […]

Newstimehub

Newstimehub

18 Mar, 2026

mini 8506 iran ta kama mutum 500 kan tuhumar leen asiri tun farkon yainta da amurka da isra ila jami i

Hukumomin Iran sun sanar da kama mutum 500 bisa zargin leƙen asiri tun bayan da Amurka da Isra’ila suka fara kai hare-hare kan ƙasar. Babban hafsan ‘yansandan ƙasar ya ce an kama mutanen ne saboda zargin ba da bayanai ga abokan gaba da kuma kafafen watsa labarai masu hamayya.

A cewarsa, akalla mutum 250 daga cikin waɗanda aka kama ana zarginsu da bai wa kafar Iran International da ke Landan bayanai, ciki har da wuraren da aka kai hare-hare. Hukumomin Iran na zargin waɗannan mutane da taimakawa wajen yaɗa bayanan sirri da kuma tada zaune-tsaye a cikin ƙasar.

An kuma danganta wasu daga cikin waɗanda ake zargin da ƙungiyoyi masu makamai da kuma ƙoƙarin tayar da tarzoma, inda jami’an tsaro suka bayyana su a matsayin masu haɗa kai da abokan gaba domin kawo cikas ga tsaro da zaman lafiya.

Kamen na zuwa ne a daidai lokacin da hare-haren haɗin gwiwa na Amurka da Isra’ila kan Iran ke ci gaba, wanda ya haddasa asarar rayuka da dama da kuma ƙara tsananta rikici a yankin. Iran ma na mayar da martani da kai hare-hare kan wasu ƙasashe da kayayyakin sojin Amurka, lamarin da ke ƙara tayar da hankulan duniya.

Tushen labari: Newstimehub