WHO: Amurka ta fita daga Hukumar Lafiya ta Duniya bayan shekara 78

Ficewar ta fara aiki daga 22 ga Janairun 2026, bayan an bi sharadin sanarwa na shekara guda bisa dokokin kasa da kasa.
23 Jan, 2026
Masana kimiyya sun gano zanen shacin hannu ‘mai shekara 67,800’ a wani kogo a Indonesia

Wani zanen shacin hannu da aka gano mai shekaru 67,800 a kogon Liang Metanduno ya shiga jerin duwatsun zane da yawa da aka gano a Tsibirin Muna kusa da tsibirin Buton da ke Kudu maso-gabashin Sulawesi.
22 Jan, 2026
Amurka ta dakatar da ba da bizar masu ƙaura ga ‘yan Nijeriya da wasu ƙasashe 74

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka a ranar Litinin ta ce ta soke biza fiye da 100,000 tun bayan dawowar Trump, wani tarihi na shekara guda.
14 Jan, 2026
Wani sanatan Amurka ya yi gargaɗi kan ƙaruwar ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa

“Ya zama wajibi a gare mu duka mu kawo ƙarshen wannan shirun mu kuma yi tur da babbar murya kan ƙyamar Musulunci da ƙin jinin Larabawa,” in ji Mark Warner.
13 Jan, 2026

Trump ya saka harajin kashi 25 kan ƙasashen da ke kasuwanci da Iran

An katse intanet da wayoyin hannu a Iran

Matar shugaban Turkiyya ta gana da shugaban UNRWA kan shirin buɗe ofis a Ankara

Burkina Faso, Mali da Nijar sun yi tir da ɗauke Maduro da Amurka ta yi

Sanatocin Republican 5 sun bi sahun ‘yan Democrat don neman sake duba ikon yaki na Trump a Venezuela
8 Jan, 2026
An kashe ɗansanda a kusa da Tehran yayin da zanga-zanga kan matsin rayuwa ta mamaye ƙasar Iran
Tun watan da ya gabata zanga-zanga ta mamaye ƙasar Iran saboda tsanantar lalacewar tattalin arziki.

8 Jan, 2026
Trump ya sanya hannu kan takardar neman cire Amurka daga ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa da na MDD
Fadar White House ta bayyana cewa akwai kungiyoyi 66 da Amurka za ta fita daga zama mamba a karkashin takardun da Trump ya sanya wa hannu, daga ciki akwai 35 da ba na MDD ba da kuma 31 a ke karkashin MDD.

7 Jan, 2026
Trump ya ƙara Nijeriya da ƙasashen Afirka 12 a jerin waɗanda za su biya $15,000 na bizar Amurka
Gwamnatin Amurka ta ninka yawan ƙasashen da ta sanya wa ‘yan ƙasarsu dole su biya kuɗin aijiya ya kai har $15,000 na samun bizar shiga kasar

7 Jan, 2026
Shugaban Rundunar Sojin Iran ya yi barazanar mayar da martani ga Trump da Netanyahu
Zan-zangar matsin tattalin arziki a Iran ta janyo hankulan kasashen duniya, ciki har da shugabannin kasashe abokan hamayya, Isra’ila da Amurka, wanda ya tilasta wa sojoji mayar da martani.

6 Jan, 2026
An sayar da kifi mai nauyin kilogiram 240 a kan Naira biliyan 4.5 ($3.2m) a Japan
An kama kifin nau’in bluefina tuna mai nauyin kilogiram 243 ne a gaɓar tekun Oma a arewa maso gabashin Japan, kuma wani kamfani Kiyomura Corp da ke cikin rukunin kantunan sayar abinci na Sushizanmai ne ya saye shi.

4 Jan, 2026
Tarayyar Afirka ta nuna ‘damuwa’, Afirka ta Kudu ta nemi a yi taron MDD da gaggawa kan Venezuela
Majalisar Dinkin Afirka da Afirka ta Kudu sun ce, hare-haren Amurka a kan Venezuela sun raina dokokin duniya.

4 Jan, 2026
Trump ya gargaɗi Colombia, ya nufi Cuba bayan ya kama Maduro
Shugaban Amurka ya ja kunnen wasu shugabannin yankin Latin Amurka bayan ya kai hare-hare Venezuela, inda ya zargi mahukuntan Bogota da laifin safarar miyagun ƙwayoyi tare da caccakar Havana game da rawar da ta taka a Caracas.

3 Jan, 2026
Amurka ba za ta bari kowa ya ci gaba daga inda Maduro ya tsaya ba – Trump
A yanzu Amurka za ta yanke shawara kan makomar Venezuela bayan “kama” Maduro”, a cewar Shugaba Trump, yana mai ƙarawa da cewa “za mu shiga cikin samar da sabon shugaba sosai.”

3 Jan, 2026
Martanin duniya na karuwa kan hare-haren da Amurka ta kai wa Venezuela
Jagorori na duniya da ‘yanmajalisar Amurka da na Birtaniya da Rasha da Tarayyar Turai suka nuna damuwa kan gagaruman hare-hare na soja sannan sun yi gargadin rikicewar lamarin da tasirinsa kan fararen hula.

3 Jan, 2026
An fitar da Shugaba Maduro da matarsa daga Venezuela, in ji Trump
Shugaban Trump ya sanar da cewa ayyukan sojin Amurka sun samu nasara a ƙasar Venezuela, inda kama Maduro da matarsa yayin wani gagarumin aikin soji.

