Cutar Ebola: Ma’aikatan lafiya 17 sun rasu yayin da cutar ke ‘yaɗuwa cikin sauri’

WHO ta yi gargaɗi cewa cutar na yaɗuwa cikin sauri duk da ƙoƙarin gaggawa da ake ƙara yi don magance kwayar cutar.

Newstimehub

Newstimehub

20 Jun, 2026

1781902398362 wbfx3e 67cadf5c6fabdd9018e57f2bb3658b4c5362edb6aec3270d9f9eb96237672e16

Wani babban jami’in Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) a ranar Jumma’a ya bayyana cewa ma’aikatan lafiya 75 a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo sun kamu da cutar Ebola sannan 17 daga cikinsu sun rasu tun bayan sabuwar ɓarkewar cutar da aka samu zuwa yanzu.

Ana tunanin Ebola ta fara yaɗuwa watanni kafin hukumomin Kongo su bayyana ɓarkewar cutar a karon farko a ranar 15 ga Mayu, ma’ana ma’aikatan lafiya da dama sun yi mu’amala da masu cutar kafin su san da ita.

Ko yanzu ma, hukumomin lafiya sun bayyana cewa kayayyakin kariya kamar safar hannu da takunkumin fuska sun kusa ƙarewa.

“Farashin da tsarin kiwon lafiya ke biya yana da tsanani sosai, domin ba mu da isassun ma’aikatan lafiya a DRC,” in ji daraktar gaggawa ta WHO, Marie Roseline Belizaire, a wata ganawar manema labarai ta hanyar bidiyo daga gabashin Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo.

WHO ta yi gargaɗi cewa cutar na yaɗuwa cikin sauri duk da ƙoƙarin gaggawa da ake ƙara yi don magance kwayar cutar.

Ta ce har yanzu tana kokarin yin gaggawa domin shawo kan matsalar da ke ƙoƙarin durƙusar da gabashin DRC.

“Barkewar cutar na nan da ƙarfinta” kuma tana “ta canzawa cikin sauri sosai”, in ji Marie-Roseline Belizaire, shugabar gaggawa ta WHO a Afirka.

‘Martani na ƙara ƙarfi’

“Duk da haka, na ga martani da ke ƙara ƙarfi a kowace rana,” kamar yadda ta shaida wa ‘yan jarida a Geneva, tana magana daga Bunia, babban birnin lardin Ituri na DRC, inda nan ne cutar ta fi ƙamari.

An ayyana ɓarkewar a ranar 15 ga Mayu, duk da cewa cutar tana ta yaɗuwa na wani lokaci ba tare da an gano ba.

Wani nau’in kwayar Ebola mai suna Bundibugyo ne ke jawo ta, wanda ba a da rigakafi ko magani na musamman dominsa.

An tabbatar da mutum 896 sun kamu da cutar a DRC kaɗai, ciki har da mutuwar mutum 232 da aka tabbatar, tare da karin sabbin mutum 21 a cikin awanni 24 da suka gabata, a cewar sabuwar sanarwar WHO.

Fiye da kashi 90 cikin 100 na waɗanda suka kamu da cutar a DRC sun kasance a Ituri, wanda rikici ya addaba.

Barkewar ta kuma yaɗu zuwa lardunan Kivu ta Arewa da Kivu ta Kudu.