An rantsar da kwamandan dakarun RSF Mohamed Hamdan Dagalo a matsayin shugaban gwamnatin adawa a Sudan.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, gamayyar ƙawancen da RSF ke jagoranta, ta ce Dagalo ya sha rantsuwar kama aiki a Nyala, babban birnin Jihar Darfur ta Kudu da ke yammacin Sudan.
Ta ce an rantsar da Abdelaziz Adam al-Hilu a matsayin mataimakin Dagalo, tare da mambobin majalisar shugaban ƙasa mai kujeru 13.
A ranar 26 ga watan Yuli ne gamayyar ƙungiyoyin suka sanar da kafa gwamnatin haɗin gwiwa, ƙarƙashin jagorancin Dagalo.
An sanya hannu kan yarjejeniyar siyasa a Kenya