An rantsar da kwamandan RSF Dagalo a matsayin shugaban gwamnatin adawa a Sudan

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, gamayyar ƙawancen da RSF ke jagoranta, ta ce Dagalo ya sha rantsuwar kama aiki a Nyala, babban birnin Jihar Darfur ta Kudu da ke yammacin Sudan.

Newstimehub

Newstimehub

1 Sep, 2025

1753640232026 axc5af 44baffcb7231547dcd6174b203897b0057a6ea7bf94a1ebefd051a607f9f780d

An rantsar da kwamandan dakarun RSF Mohamed Hamdan Dagalo a matsayin shugaban gwamnatin adawa a Sudan.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, gamayyar ƙawancen da RSF ke jagoranta, ta ce Dagalo ya sha rantsuwar kama aiki a Nyala, babban birnin Jihar Darfur ta Kudu da ke yammacin Sudan.

Ta ce an rantsar da Abdelaziz Adam al-Hilu a matsayin mataimakin Dagalo, tare da mambobin majalisar shugaban ƙasa mai kujeru 13.

A ranar 26 ga watan Yuli ne gamayyar ƙungiyoyin suka sanar da kafa gwamnatin haɗin gwiwa, ƙarƙashin jagorancin Dagalo.

An sanya hannu kan yarjejeniyar siyasa a Kenya