Gwamnatin Ghana ta yi watsi da gudunmawar cedi miliyan 20 daga kamfanin MTN

Koda yake gwamnatin ta yaba wa MTN saboda wannan tsari da ‘kyakkyawar niyya,’ ta bayyana cewa gwamnati ta ƙi karaɓr kuɗin ne saboda ta riga ta fitar da isassun kuɗaɗen gudanar da aikin kwashe ‘yanƙasar da kuma sake tallafa wa gina rayuwarsu a gida.
26 Aug, 2026
Nijar ta cim ma yarjejeniyar gina tashar samar da wutar lantarki ta hasken rana mai karfin MW 200

Za a kwashe tsawon shekaru 20 ana aiki karkashin yarjejeniyar, kana wani kamfani mai zaman kansa ne zai gina cibiyar tare da gudanar da ayyukanta kafin daga karshe ya mika wa gwamnatin Nijar, in ji wani rahoto.
26 Aug, 2026
Gwamnatin Ghana za ta kawo ƙarshen binciken da ‘yansanda ke yi na ababen hawa a kan hanya

A ƙarkashin sabon tsarin, za a yi amfani da kyamarori da na’urar tattara bayanai da ɗaukar hoto don gano laifuka a yayin zirga-zirgar ababen hawa, kuma gwamnatin Ghana za ta haɗa-gwiwa da Sashen Kula da Sufuri da Motoci (MTTD) don cim ma matakin.
25 Aug, 2026
Mutane akalla 30 sun mutu sakamakon ruftawar wani babban wurin tara bola a Guinea

Tuni aka aika da ma’aikatan agajin gaggawa wani babban wuri tara bola da ya rufta a babban birnin Guinea bayan mamakon ruwan sama, lamarin ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.
24 Aug, 2026

Yadda na tsira daga kifewar jirgin Sokoto da ya kashe mutum fiye da 60—Hakimi

Shugaba Paul Biya ya koma Kamaru bayan ya shafe kwanaki 73 ba ya nan

Ɗaruruwan mayaƙan RSF ciki har da kwamandoji sun sauya sheka zuwa Rundunar Sojin Sudan

Zaftarewar ƙasa a wajen haƙar ma’adinai ta yi ajalin mutum aƙalla 100 a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya

Nijeriya ta kama wani fitacce a shafukan sada zumunta bayan badaƙalar hodar iblis ta dala miliyan 29
18 Aug, 2026
Hakainde Hichilema ya lashe zaben shugaban kasar Zambia karo na biyu
Shugaban Zambia Hakainde Hichilema ya doke babban abokin hamayyarsa a zaɓen shugaban ƙasa na ranar Alhamis ɗin da ta gabata bayan ya samu ƙuri’u miliyan 2.9, inda abokin hamayyarsa Brian Mundubile ya samu ƙuri’u miliyan 1.8.

16 Aug, 2026
Nijar da wani kamfani sun ƙulla yarjejeniyar gina matata mai tace gangar mai 100,000 a yini
Ya ƙara da cewa matatar za ta kawo ƙarshen dogaron Nijar kan mai daga ƙetare, yana mai ƙarawa da cewa abin da Nijar ba ta sha ba daga man za a fitar da shi ƙasashe maƙwabta a yankin.

15 Aug, 2026
Sojin Sudan ta yarda da ‘zaman lafiya ta gaskiya’ ba tare da RSF ta ƙwace iko ba, in ji Janar Burhan
Babban hafsan sojin Sudan Abdel Fattah al-Burhan ya ce dole a fara zaman lafiyar da ajiye makaman rundunar RSF da kuma dawo da tsaro da rayuwar yau da kullum.

14 Aug, 2026
Shugaban Chadi Déby ya yi afuwa ga jagoran hamayya da ke ɗaure, Success Masra
Ana sa ran za a saki Masra tare da wasu ‘yansiyasa takwas.

14 Aug, 2026
Mali ta yi afuwa ga wani dan Faransa ake zargi da yunkurin kitsa juyin mulki a kasar
Gwamnatin riƙon kwarya ta Mali ta yi afuwa ga wani ɗan ƙasar Faransa wanda ke zaune a gidan yari bayan an yanke masa hukuncin ɗauri na shekara 20 bisa zargin ƙulla makircin kifar da gwamnatin ƙasar, kamar yadda hukumomi suka sanar a ranar Alhamis.

12 Aug, 2026
Afirka ta Kudu ta buƙaci ƙasashen Afirka da ta mayar da jama’arsu gida su biya ta ladan jigila
Afirka ta Kudu na buƙatar gwamnatocin sauran ƙasashen Afirka da dama su biya ta kuɗaɗen da ta kashe wajen jigilar dubban ‘yan ƙasashensu zuwa gida.

12 Aug, 2026
Sojojin Sudan sun dakile hare-haren jiragen yaki maras matuka na RSF a Khartoum da Kogin Nilu
Hare-haren jiragen sama marasa matuƙa na RSF na baya-bayan nan sun mayar da hankali kan wuraren soji da muhimman kayayyakin more rayuwa a biranen da sojoji ke rike da ikonsu a Sudan.

12 Aug, 2026
Yankuna uku na Ghana za su fuskanci katsewar wutar lantarki, in ji kamfanin ECG
Katsewar wutar na daga wani ɓangare na ayyukan gyara da kamfanin ya tsara da nufin ƙara ingancin wutar lantarki.

10 Aug, 2026
Fiye da mutum 5000 sun tsere saboda rashin tsaro da ke daɗa ƙamari a Darfur ta Yamma a Sudan: MDD
Da yawa daga cikin iyalan da lamarin ya shafa sun kasance waɗanda aka tilasta musu barin gidajensu ne kuma suka ƙetare zuwa cikin, in ji hukumar IOM ta Majalisar Dinkin Duniya.

9 Aug, 2026
Hatsarin mota ya kashe mutum 22, ciki har da sojoji 17 a Nijar
Minsitan Sufurin ƙasar Kanal-Manjo Abdourahamane Amadou ya ce zai gayyaci kamfanonin STM da SONITRAV, waɗanda a tsakanin motocinsu ne hatsarin ya auku, su bayyana a ofishinsa ranar Litinin



