Iran ta ce ta yi nasara a ‘yaƙi da kuma diflomasiyya’ bayan Trump ya nemi a yi saranda

Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, a ranar Talata ya bayyana cewa Iran ta “yi nasara a yaƙi da kuma diflomasiyya,” inda ya ce waɗanda da farko suka nemi Tehran ta “miƙa wuya ba tare da wani sharadi ba,” daga baya sun koma neman sulhu.

Newstimehub

Newstimehub

18 Aug, 2026

a4f6804d 2606 4a5c 8da4 b8d896c9fde1 1775660251191

Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, a ranar Talata ya bayyana cewa Iran ta “yi nasara a yaƙi da kuma diflomasiyya,” inda ya ce waɗanda da farko suka nemi Tehran ta “miƙa wuya ba tare da wani sharadi ba,” daga baya sun koma neman sulhu.

Da yake magana a wani taro, Araghchi ya ce Iran ta yi tsayin daka na tsawon kwanaki tana fuskantar abin da ya bayyana a matsayin “babbar rundunar soji mafi ƙarfi a duniya,” wadda kuma wata rundunar da ke ikirarin tana da ƙarfin soji ta goyi bayanta, tare da kusan dukkan ƙasashen Yamma da wasu ƙasashe da dama daga cikin yankin da wajensa, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Tasnim ya ruwaito.

“Waɗanda suke neman Iran ta miƙa wuya ba tare da wani sharadi ba, jim kaɗan bayan fara yaƙin, su ne suka roƙi a yi shawarwari,” in ji Araghchi.

Ya yi ikirarin cewa Tehran da farko ta ƙi amincewa da tsagaita wuta, ta kuma ci gaba da yaƙi har sai da aka kai wani matsayi da ɗayan ɓangaren ya amince da tsagaita wuta da kuma yin shawarwari “bisa sharuddan Iran.”

“Mun yi yaƙi da ƙarfinmu, kuma mun jajirce wurin tattaunawa,” in ji shi, yana ƙarawa da cewa ministocin harkokin wajen ƙasashe da dama sun gaya masa cewa: “Kun yi nasara a yaƙin da kuma diflomasiyya.”

Kalaman Araghchi sun zo ne bayan da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi kira ga Iran a ranar Litinin da ta daina yaƙin ta kuma “ɗaga farar tuta.”