Gwamnatin Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 na tsawon kwanaki 15 bisa zargin ɓoye siminti mai yawa domin haddasa ƙarancinsa a kasuwa tare da tayar da farashinsa, kamar yadda Ma’aikatar Kasuwanci da Masana’antu ta bayyana.
Ministan Kasuwanci da Masana’antu, Abdoulaye Seydou, ya sanya hannu kan umarnin dakatarwar inda aka hana dillalan saye ko sayar da siminti.
Haka kuma, gwamnati ta haramta zirga-zirgar manyan motocin dillalan a faɗin ƙasar.
Ma’aikatar ta ce dillalan sun karya dokokin goyayya na ƙasar ta hanyar ɓoye adadi mai yawa na siminti duk da shirin gwamnati na sayar da siminti a farashi mai rangwame domin sauƙaƙa wa jama’a samun kayan gini.
Gwamnatin ta yi gargaɗin cewa za a iya gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu, tare da jaddada cewa za ta ci gaba da yaƙi da masu haddasa tashin farashi da duk wata haramtacciyar harka a fannin kasuwancin siminti.
A farkon wannan watan ma, hukumomi sun ba da umarnin ƙwace simintin da aka samu yana da alaƙa da haramtattun mu’amaloli tare da miƙa shi ga Asusun Haɗin Kan Kasa na Kare Ƙasa (FSSP).
Ƙungiyoyin kare haƙƙin masu saye sun yi maraba da matakin, suna mai cewa zai taimaka wajen hana ƙarancin siminti da kuma daidaita farashinsa.















