Fitaccen ɗan siyasar Rached Ghannouchi, jagoran jam’iyyar Ennahda a Tunisia, an kai shi asibiti bayan lafiyarsa ta tabarbare yayin da yake tsare. Jam’iyyarsa ta ce lamarin ya tsananta sosai har sai da aka bukaci kulawar gaggawa, kuma yanzu yana karkashin sa ido na likitoci.
Ƙungiyar Ennahda ta bayyana cewa tsare shi ba bisa ka’ida ba ne, tana mai kira da a sake shi cikin gaggawa. Ta kuma ce wasu masana na kasa da kasa, ciki har da wata ƙungiya ta Majalisar Dinkin Duniya, sun taba nuna cewa tsare shi yana da alaƙa da ra’ayinsa na siyasa ba wai laifi ba.
An kama Ghannouchi ne a watan Afrilu na 2023 bayan jami’an tsaro sun kai samame gidansa. Tun daga lokacin, an yanke masa hukunci a shari’o’i da dama, ciki har da zargin tayar da rikici da samun kudade daga kasashen waje. A shekarar 2026, an sake yanke masa hukuncin daurin shekaru 20 tare da wasu jagororin jam’iyyar.
Magoya bayansa na cewa shari’o’in na da nasaba da siyasa, suna zargin gwamnatin shugaban ƙasa Kais Saied da kokarin murkushe masu adawa. Sai dai gwamnati na dagewa cewa bangaren shari’a mai zaman kansa ne, kuma ana gudanar da komai bisa doka.
Kungiyoyin kare hakkin bil’adama da masu adawa da gwamnati na ci gaba da nuna damuwa, suna ganin wannan na daga cikin matakan da ake dauka don takaita ’yancin fadin albarkacin baki a Tunisia.
A halin yanzu, Ghannouchi na ci gaba da karbar magani, yayin da rikicin siyasa da na shari’a ke kara tsananta a kan lamarinsa.
MAJIYAR LABARI: NEWSTIMEHUB













