Ministan kuɗin Qatar, Ali Ahmed Al-Kuwari, ya gargaɗi cewa nan ba da jimawa ba duniya za ta fara jin cikakken tasirin yaƙin Iran.
Ya ce hauhawar farashi da ake gani yanzu ƙanƙanin ɓangare ne, inda ya yi hasashen cewa cikin wata ɗaya ko biyu za a fuskanci babbar matsala ta tattalin arziki.
Ya kuma yi gargaɗin cewa za a iya samun ƙarancin makamashi, ba wai tsadar sa kaɗai ba, tare da yiwuwar matsalar abinci sakamakon raguwar samar da taki.
Sai dai ya tabbatar da cewa Qatar na da ƙarfin jure wa matsin lambar na tsawon shekara guda saboda ajiyar kuɗinta da tsare-tsaren tattalin arziki.
Tushen labari: Newstimehub














