Jumullar mutum 246,228 ne da kuma gidaje 32,251 ambaliyar ruwa ta shafa a Jamhuriyar Nijar sakamakon ruwan saman da aka fara tun daga farkon damina.
Kwamitin Kula da Bayar da Kariya ga Ambaliya a Nijar ne ya tabbatar da waɗannan alƙaluma a yayin taronsa na huɗu da aka gudanar a ranar Juma’a, 12 ga Satumbar 2025 a ɗakin taro na ofishin Firaminista.
A cewar kwamitin, zuwa yanzu, ambaliyar ta shafi unguwanni da ƙauyuka 1,009 a cikin ƙananan hukumomi 122, yayin da “tallafin da aka bayar zuwa 2 ga Satumbar 2025 ya kai ga gidaje 18,962 da suka ƙunshi mutum 142,642 tare da tan 1,896.2 na hatsi a cikin tallafin da aka bayar sau uku”.
“An bayar da umarni na musamman domin tabbatar da cewa tallafin ya kai ga waɗanda suke da bukatarsa,” in ji majiyar.