‘Yan sanda za su yi bincike kan harin da aka kai wa ayarin motocin Abubakar Malami a Kebbi

A ranar Litinin ne wasu da ake zargin ‘yan daba ne suka kai wa ayarin motocin Malami hari, a daidai lokacin da rahotanni ke cewa mutane da dama sun koma jam’iyyar haɗaka ta ADC da tsohon Ministan Shari’ar ke daga cikin manyan jagororinta.

Newstimehub

Newstimehub

2 Sep, 2025

7098b329de13a8b2c79939ad1ddd126050bca1d126df02ea2a746ce09a6abc14

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kebbi, Muhammad Sani Bello ya ce ba wanda aka kama zuwa yanzu dangane da harin da aka kaiwa ayarin motocin tsohon Ministan Shari’a na Nijeriya, Abubakar Malami.

CP Bello ya shaidawa manema labarai bayan wani taron tsaro da gwamnan jihar ya yi, cewa lamarin da ya faru a kewayen unguwar GRA, yana da alaƙa da wasu ‘yan daba ne masu alaƙa da wata ƙungiyar siyasa.

Kwamishinan ya ƙara da cewa, wasu ‘yan siyasa ma suna karya dokar hana amfani da jiniya da kuma yin yaƙin neman zaɓe ba tare da izini ba.

Ya bayyana cewa an samar da matakan tsaro domin tabbatar da bin doka da oda, yayin da ya yi kira ga jam’iyyun siyasa da su kwantar da hankalinsu.

Ya jaddada cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kuma duk wanda aka samu da laifi za a kama shi tare da gurfanar da shi a gaban ƙuliya.