Ambaliyar ruwa ta rusa gidaje a ƙauyuka da dama na Sudan

Ɗaruruwan mutane sun rasa muhallansu a Jihar River Nile sannan gomman gine-gine sun rushe sakamakon ruwan sama mai ƙarfi.

Newstimehub

Newstimehub

28 Aug, 2025

1756362525898 6wps7u 0f4031b9b7cd6c55141557cd5ddfe75b97d56c14f619de8ade46e0e8a066ac66

Akalla mutane 14 sun rasa rayukansu sakamakon ruwan sama mai karfi da ambaliyar ruwa a arewaci da kudu maso gabashin Sudan, kamar yadda kafafen yada labarai na cikin gida suka bayyana a ranar Laraba.

Shaidu sun ce ruwan sama mai ƙarfi da ambaliyar ruwa sun lalata garuruwa da ƙauyuka da dama a Jihar River Nile, wanda ya haifar da katsewar wutar lantarki da kuma rushewar gine-gine da dama, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na jihar, SUNA, ya ruwaito.

Mutane shida sun rasu lokacin da gidaje suka rushe sakamakon ruwan sama mai ƙarfi a arewacin Jihar River Nile.

Wata uwa da ‘ya’yanta uku sun mutu a Jihar Sennar da ke kudancin Sudan bayan ɗakin gidansu ya rushe sakamakon ruwan sama mai karfi.

Mutane sun rasa matsuguni