Fidan da Rubio sun yi nazarin sakamakon tattaunawar Washington kan kawo ƙarshen yaƙin Ukraine

Ministan Harkokin Wajen Turkiya Hakan Fidan da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio sun tattauna kan matakan da za a iya bi don kammala yaƙi tsakanin Rasha da Ukraine.

Newstimehub

Newstimehub

20 Aug, 2025

63ec7c3a5b5d74cfbc55de750d76f59300ac08109c5617ec6615f6ab0c1bfa56

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, da Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio, sun tattauna kan sakamakon taron da aka gudanar a birnin Washington tsakanin Shugaban Amurka Donald Trump da Shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy da sauran Shugabannin Turai.

A wata tattaunawar wayar tarho da suka yi a ranar Talata, sun kuma tattauna kan sakamakon taron da aka yi tsakanin Shugaban Amurka Donald Trump da Shugaban Rasha Vladimir Putin a Alaska a ranar 15 ga watan Agusta, kamar yadda majiyoyin diflomasiyyar Turkiyya suka bayyana.

Sun yi magana kan matakan da za a iya dauka nan gaba don kawo karshen yakin da ke tsakanin Rasha da Ukraine, inda Fidan ya bayyana cewa a shirye Turkiyya take ta bayar da duk wani irin tallafi don cim ma zaman lafiya mai adalci da ɗorewa.

A cewar mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, Tommy Pigott jami’an biyu sun amince kan bukatar dakatar da kashe-kashe tsakanin kasashen biyu da ke fada.

Ci gaba da goyon bayan zaman lafiya a Ukraine

Mataimakin Shugaban Turkiyya, Cevdet Yilmaz ya bayyana a ranar Talata cewa Turkiyya za ta ci gaba da goyon bayan shirye-shiryen diflomasiyya da nufin cim ma “zaman lafiya mai adalci da ɗorewa” a Ukraine.

“Za mu ci gaba da bayar da cikakken goyon baya ga kokarin diflomasiyya don zaman lafiya mai adalci da dorewa,” in ji Yilmaz a dandalin sada zumunta na Turkiyya, NSosyal.