‘Yan bindiga sun kashe mutum 13 a yayin da suke sallah a masallaci a Jihar Katsina

Lamarin ya faru ne a yayin da ake sallar asuba, lokacin da ‘yan bindigar ɗauke da muggan makamai suka dirar wa masallatan tare da buɗe musu.

Newstimehub

Newstimehub

19 Aug, 2025

4918fc3ca79c472f367cebc59cbebebc320af1924ae53876e8c539932f83df5b

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a Unguwan Mantau da ke karamar hukumar Malumfashi a jihar Katsina, inda suka kashe masu ibada 13.

Lamarin ya faru ne a yayin da ake sallar asuba, lokacin da ‘yan bindigar ɗauke da muggan makamai suka dirar wa masallatan tare da buɗe musu.

Rahotanni sun ce maharan sun kai harin ne bayan da a baya bayan nan al’ummar garin suka fatattake su har sau biyu.

Gidan talabijin na Channels TV ya rawaito Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Dr. Nasiru Mu’azu cewa ya tabbatar da lamarin a wata sanarwa a ranar Talata, inda ya bayyana harin “da na ramuwa da ‘yan bindigar suka kai bayan da a baya mazauna garin suka fatattake su.”

Kwamishina Mu’azu ya ce gwamnatin jihar Katsina tuni ta sanar tura ƙarin tsaro da ɗaukar matakan kariya bayan faruwar mummunan lamarin.

Ya ce a yanzu haka akwai jami’an tsaro jibge a Unguwan Muntau don kwantar da hankula.

“Abin ya faru ne a lokacin da ɓata garin suka ƙaddamar da harin ramuwa a kan al’ummar, Al’ummar Musulmai na salla a masallacin da asuba a lokacin da ‘yan ta’addan suka fara harbin kan mai uwa da wabi a masallacin.