Turkiyya, Masar sun haɗa kai don magance rikicin yankinsu, sun yi watsi da shirin sake mamaye Gaza

Ƙasashen biyu sun sha alwashin haɗa gwiwa a yunƙurin shawo kan ƙalubalen da yankin Gabas ta Tsakiya yake fama da shi, a cewar Ministan Harkokin Wajen Masar.

Newstimehub

Newstimehub

10 Aug, 2025

a3ac7568ea1bf4b77dd34e25857156231cf93e9bd621b6d0b6c7b5527c4c6463

Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdelatty ya sanar ranar Asabar cewa suna haɗa gwiwa da Tukiyya a hanyoyin warware rikice-rikicen da ke addabar yankin, bayan ganawar da ya yi da Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan a El Alamein, Masar.

A wani taron manema labarai na haɗin gwiwa, Abdelatty ya bayyana halin da ake ciki a dangantakar Masar da Turkiyya a matsayin “muhimmin mataki na alaƙa mai ƙarfi.”

Ministocin biyu sun tabbatar da “amincewa da yunƙurin haɗa kai tare da yin amfani da dukkan dama wajen tunkarar shirin Isra’ila na mamaya da kuma tasirinsa,” in ji shi.

Taron gaggawa na OIC

Fidan ya ce Turkiyya za ta kira taron gaggawa na Ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmai wato Organization of Islamic Cooperation (OIC) domin tattauna shirin Isra’ila na cikakkiyar mamaya a Gaza.