Rahoton United Nations Development Programme ya nuna cewa yaƙin Iran da United States da Israel ke yi na iya rage tattalin arzikin ƙasashen Larabawa da har kashi 6%.
Rahoton ya ce yankin na iya fuskantar asarar dala biliyan 120 zuwa 194, yayin da kasuwanci da zuba jari ke raguwa sakamakon tangardar jigilar kaya da tashin farashin sufuri.
Haka kuma, ana hasashen kusan mutane miliyan 4 za su ƙara fadawa cikin talauci, yayin da miliyan 2.5 zuwa 3.5 za su rasa ayyukansu, musamman ma’aikata marasa ƙwarewa.
Ƙasashen Gulf da yankin Levant ne za su fi fuskantar illa, yayin da wasu ƙasashen arewacin Afirka za su iya amfana daga tashin farashin mai.
Rahoton ya ƙara da cewa rikicin ya riga ya haddasa tashin farashi da tangarda a harkokin kasuwanci, musamman bayan rufe Strait of Hormuz da kuma hare-haren jiragen ruwa.
Tushen labari: Newstimehub














