Tinubu ya yi alƙawarin hanzarta ƙera makamai da harsasai a cikin Nijeriya saboda tsaro

Shugaba Tinubu wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Kashim Shettima a Kwalejin Tsaro ta Nijeriya da ke Abuja, ya yi alkawarin hanzarta ƙera makamai da harsasai a cikin gida domin ƙarfafa tsarin tsaron ƙasar da kuma rage dogaro da ƙasashen waje.

Newstimehub

Newstimehub

23 Aug, 2025

184b9bf3509eb84b17dffd5742363975893bf930e3cb6d441ebd84ecf4c9b821

Shugaba Bola Tinubu a ranar Juma’a ya yi alkawarin hanzarta ƙera makamai da harsasai a cikin gida domin ƙarfafa tsarin tsaron Nijeriya.

Yayin da yake jawabi a Abuja a lokacin bikin kammala karatun Course 33 na Kwalejin Tsaro ta Nijeriya da ke Abuja, wanda mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta.

Ya bayyana cewa ƙara ƙarfin masana’antu na cikin gida zai rage dogaro da masu kaya na ƙasashen waje, sannan zai inganta yaki da rashin tsaro a ƙasa.

Daliban na Course 33 sun fito ne daga sojojin ƙasa da na ruwa da na sama  na Nijeriya da sauran hukumomi daga ciki da wajen Nijeriya.

Shugaban ya nuna farin ciki da taken na Course 33 na kwalejin, “Karfafa Hukumomi Don Tsaro da Ci Gaban Nijeriya,” yana mai cewa tushe na kowace al’umma mai nasara shi ne hukumomi masu ƙarfi da juriya.