Tinubu ya amince a sayi ƙarin jirage mara matuƙa don yaƙi da ‘yan bindiga a Arewacin Nijeriya

Kwanan baya ne Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya halarci baje-kolin kayayyakin yaƙi da ƙere-ƙere na duniya a Istanbul inda Turkiyya ta amince ta sayar da ƙarin jirage mara matuƙa da horas da sojojin Nijeriya kan dabarun yaƙi na zamani.

Newstimehub

Newstimehub

3 Sep, 2025

30fa9fa18826fb62ed7958e59aebdb2c7cdf8bc90d5cdad1ddb99ed456973283

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya ce amince ma’aikatar tsaron ƙasar ta sayi ƙarin jirage mara matuƙa domin yaƙi da ‘yan bindiga a Jihar Katsina da sauran sassan ƙasar.

Wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata da maraice ta ce shugaban na Nijeriya ya kuma bayyana cewa za a ƙara yawan dakaru a Jihar Katsina domin hana kai hare-hare kan ‘yan ƙasa da ba su ji ba ba su gani ba.

Shugaban ya bayyana wannan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawagar manyan ‘yan jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin gwamnan jihar Dikko Umaru Radda.

Sanarwar ta ambato Shugaba Tinubu yana cewa: “Yau na ba da umarni ga dukkan jami’an tsaro su ƙarfafa [ayyukansu] su kuma sake nazari kan dabarun yaƙi. Mun amince a sayi ƙarin jirage mara matuƙa.”

Ƙalubalen da muke fuskanta abubuwa ne da za mu iya cin galaba a kansu. Da gaske muna da iyakoki da babu tsaro. Mun gaji da wannan rauni, ya kamata a ce an magance wannan matsala kafin yanzu. Ƙalubale ne da ya zama dole mu magance shi, kuma muna tunkararsa,” in ji Tinubu.