Dakarun Rundunar Haɗin Gwiwa ta Arewa Maso Gabas ta Operation Hadin Kai sun kashe wasu mutum 12 da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram/ISWAP ne a wasu jerin samame da suka kai a wurare daban-daban na Ƙaramar Hukumar Mafa a Jihar Borno.
Ƙaramar Hukumar Mafa na da nisan kusan kilomita 59.8 daga Maiduguri, babban birnin jihar.
Sojojin sun samu nasara ne bayan sun samu bayanan sirri da kuma bayanai daga na’urorin leƙen asiri na Rundunar Sojin Sama, waɗanda suka samar da bayanai kai tsaye domin aiwatar da luguden wuta kan ‘yan ta’addan.
Wannan haɗin gwiwar ya kai ga kwato sansanonin ’yan ta’adda a yankunan.