Sojojin Nijeriya sun kashe ’yan ta’adda 12 a Mafa da ke Borno

Sojojin sun samu nasara ne bayan sun samu bayanan sirri da kuma bayanai daga na’urorin leƙen asiri na Rundunar Sojin Sama, waɗanda suka samar da bayanai kai tsaye domin aiwatar da luguden wuta kan ‘yan ta’addan.

Newstimehub

Newstimehub

1 Sep, 2025

1a4f9b4c1c9c1a6c3bc5bc012fa875559124e619335e24c4c9e066d273eb5bdd

Dakarun Rundunar Haɗin Gwiwa ta Arewa Maso Gabas ta Operation Hadin Kai sun kashe wasu mutum 12 da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram/ISWAP ne a wasu jerin samame da suka kai a wurare daban-daban na Ƙaramar Hukumar Mafa a Jihar Borno.

Ƙaramar Hukumar Mafa na da nisan kusan kilomita 59.8 daga Maiduguri, babban birnin jihar.

Sojojin sun samu nasara ne bayan sun samu bayanan sirri da kuma bayanai daga na’urorin leƙen asiri na Rundunar Sojin Sama, waɗanda suka samar da bayanai kai tsaye domin aiwatar da luguden wuta kan ‘yan ta’addan.

Wannan haɗin gwiwar ya kai ga kwato sansanonin ’yan ta’adda a yankunan.