Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya fara hutun shekara-shekara ranar Alhamis 4 ga watan Satumba na wannan shekarar.
Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Nijeriya, Bayo Onanuga, ya wallafa a shafinsa na X, ta ce shugaban zai shafe kwanakin aiki goma yana hutun na shekara-shekara.
“Shugaba Tinubu zai yi hutun ne tsakanin Faransa da Birtaniya kana ya dawo ƙasar [Nijeriya],” in ji sanarwar.
Daga bisani shugaban na Nijeriya ya tashi daga Abuja inda ya nufi Turai a jirgin shugaban ƙasa.