Rundunar Sojin Ghana za ta yi cikakken bincike kan hatsarin helikwafta – Mahama

Shugaban ƙasar ya ce za a yi wa waɗanda suka mutu a hatsarin jana’iza ta ƙasa.

Newstimehub

Newstimehub

8 Aug, 2025

9e1efbf9c3cb8da671ee71d0b4f205a38dc77c406c7fe102e8279b443fb99b8c

Shugaba John Mahama ya tattabar wa mutanen ƙasarsa cewa rundunar sojin ƙasar za ta gudanar da cikakken bincike kan abin da ya janyo hatsarin helikwaftan da ya kashe ministoci biyu da wasu jami’a gwamnatin Ghana. 

Da yake jawabinsa na farko tun bayan hatsarin a fadar gwamnatin ƙasar ranar Alhamis, Shugaba Mahama ya bayyana alhininsa tare da miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda lamarin ya rutsa da su

Ya ce duk da cewa al’umar ƙasar na son sanin abin da ya janyo hatsarin, ya kamata ‘yan ƙasar su haɗa kai a wannan lokacin makokin. 

“Yayin da muke juyayi, dole mutane za su yi ta tambaya game da silar wannan bala’in kuma [tambayoyin] na da muhimmanci.,” in ji shi.

Shugaba Mahama ya jaddada jajircewar gwamnatin wajen gano gaskiyar abin da ya janyo hatsarin, yana mai tabbatar wa ‘yan ƙasar Ghana cewa babu wani bayanin da za a ɓoye musu.