14 Feb, 2026

‘Yanbindiga sun kashe DPO na ‘yansandan Nijeriya a Jihar Katsina

Jami’in ɗansandan ya rasu ne bayan bindigarsa ta samu matsala a yayin musayar wuta da ‘yanbindiga a yankin Karamar Hukumar Rimi ta Jihar Katsina.

1771061168564 s3mis 224f68ab2ef928dd1199c81f65624d80342f6cf701d7da825dadcde73bcca131

13 Feb, 2026

‘Rashin sake wa hukumomin gwamnatin Nijeriya kuɗaɗen kasafi koma-baya ne ga ci gaban ƙasa’

A farkon makon ne Ministan Lafiya na Kasar Farfesa Mohammed Ali Pate ya koka kan naira miliyan 36 da aka bai wa ma’aikatarsa daga cikin naira biliyan 218 da aka ware mata a kasafin kudin shekarar 2025.

2025 10 09t155555z 1 lynxnpel980u8 rtroptp 3 nigeria naira investors

13 Feb, 2026

INEC na neman naira biliyan 873 don gudanar da zaɓukan shekarar 2027

Shugaban hukumar INEC ya ce kasafin kudin hukumar ta shekarar 2026 zai ɗauki nauyin ayyukan hukumar na yau da kullum, ciki har da zaɓukan cika-gurbi da waɗanda za a yi bayan lokacin zaɓukan ƙasa.

b11d132f0bc59b332fbc8c815d0fd021590f00073926ff1367ffad26c7c37d0d main

12 Feb, 2026

Jami’an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa’i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi

Mai taimaka wa tsohon gwamnan kan yada labarai Muyiwa Adekeye ya wallafa a shafinsa na X cewa a ranar Alhamis cewa “A yau jami’an tsaro sun so su kama Nasir El-Rufai bayan komawarsa gida daga birnin Cairo.

781a6a695ec335c9c61c765bbc4399f4dcebedfe8dabf4a870c7e8d20d8cbe1f

11 Feb, 2026

Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan Boko Haram 16 a Borno

Dakarun sojin sun daƙile yunƙurin harin na ‘yan ta’addan da ƙarfin makamai da dabarun yaƙinsu, in ji rundunar ta Operation Hadin Kai.

26a73c22fd49e3a70a49ccf3c4bf5d0385cb1cc674d6d9d3d3ac7a977d018f15

11 Feb, 2026

Amurka za ta tura sojojinta 200 Nijeriya

Tura sojojin za ta faɗaɗa haɗin kan soji tsakanin Washington da Abuja, inda za su mayar da hankali kan horaswa da bayar da bayanan sirri da haɗa kan ayyuka na sojojin sama da ƙasa ba tare da bai wa Amurka damar shiga yaƙin kai-tsaye ba.

ac73b79f621b79f31560f34de26e31c06b895fae134ed8b512765f9a4a244d41

10 Feb, 2026

Sojojin Nijeriya sun kashe gomman ‘yan-ta’adda, sun dawo da mutum 700 gida a arewa maso gabas

Yankin arewa maso-gabas na Nijeriya ya kasance cibiyar rikicin ‘yan-ta’adda tsawon sama da shekaru 10, wanda Boko Haram da ISWAP suka haddasa.

2026 02 05t135403z 1822892137 rc2pfjauc41i rtrmadp 3 nigeria security

10 Feb, 2026

Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan ya ajiye aikinsa

Kawo yanzu dai ba a bayyana dalilin murabus ɗin ba, amma kafofin watsa labaran Nijeriya sun ambato Ahmed Muazu, mai magana da yawun shugaban yana tabbatar da batun.

7fa1cd74307b997552bc7c5a81001edcd3eb742de55e3a8d724a9e2dc2f0e6f4

9 Feb, 2026

Mutum fiye da 30 sun rasu sakamakon hatsarin mota a Jihar Kano

Gwamnan ya ba da umarnin cewa a yi wa duk waɗanda suka ji rauni a hatsarin magani kyauta a asibitin gwamnati

kano 20001

8 Feb, 2026

Nijeriya: ‘Yanbindiga sun sace wani faston Katolika a Kaduna, sun kashe mutum uku

Cocin Katolika reshen Kafanchan ta ce mutum goma ne aka sace, amma ‘yansanda sun ce biyar ne, sannan mutanen da aka kashe biyu sojoji ne ɗaya kuma ɗansanda.

2026 01 20t171019z 1638829413 rc2y4jan0rrh rtrmadp 3 nigeria security
Loading...