Nijeriya ta ƙaddamar da sabuwar manhajar karatu a matakin farko da babbar sakandare da ilimin fasaha

“Sabon tsarin zai kawo daidaito a darussan da ake koyarwa wajen zurfafawa da kuma koyar da ilimi a aikace.

Newstimehub

Newstimehub

1 Sep, 2025

f551e643b1cbc7e8c3536df636f525287c1c643bded28c5fb2fd2799a9e610b8

Gwamnatin Nijeriya ta kammala nazari mai zurfi kan manhajoji karatu a fannin ilimi a matakin farko da na manyan makarantun sakandire da kuma fannin fasaha, da nufin rage lafta karatu da kuma inganta tsarin koyarwa.

Sabuwar manhajar za ta fara ne a wannan shekarar karatun ta 2025/2026.

Da take sanar da matakin a madadin Ministan Ilimi Dakta Maruf Tunji Alausa, Karamar Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sai’d Ahmad, ta ce an gudanar da bitar ne tare da hadin gwiwar Hukumar Bincike da Cigaban Ilimi ta Nijeriya (NERDC), da hukumar ilimin bai-ɗaya a matakin farko Universal Basic Education Council UBEC, da NSSEC, da NBTE, da sauran masu ruwa da tsaki.

“Sabon tsarin zai kawo daidaito a darussan da ake koyarwa wajen zurfafawa da kuma koyar da ilimi a aikace.