Ma’aikatar Shari’ar Nijar ta yi bayani game da rushe ƙungiyoyin ƙwadago

Kamfanin dillancin labaran Nijar(ANP) ya ambato wata sanarwar da ministan shari’ar ƙasar, Alio Daouda, ya fitar tana cewa an yi ammanar cewa ƙungiyoyin ƙwadagon huɗu ba sa aiki domin inganta aikin ɓangaren shari’a domin kare muradun al’umma.

Newstimehub

Newstimehub

11 Aug, 2025

2e09acb3ce1777e4fd6ac9a114faa18563ad3bb608789c40ee64db8c5f132312

Ma’aikatar Shari’ar Jamhuriyar Nijar ta yi bayani game da matakin da gwamnatin ƙasar ta ɗauka na rusa ƙungiyoyin ƙwadago huɗu da ke fannin shari’a.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar, (ANP) ya ambato wata sanarwar da Ministan Shari’ar ƙasar, Alio Daouda ya fitar tana cewa an yi amannar cewa ƙungiyoyin ƙwadagon huɗu ba sa aiki domin inganta aikin ɓangaren shari’a domin kare muradun al’umma.

Ƙungiyoyin ƙwadagon sun haɗa da ƙungiyoyin SAMAN da SNAJ da SYNCAT da kuma UMAN.

Sanarwar ta ƙara da cewa maimakon ƙoƙarin kare muradun al’umma, ƙungiyoyin na aikin kare muradun kansu ne, lamarin ke ƙasa-ƙasa da harkar yi wa ƙasa hidima.