Jam’iyyar Adalci da Ci Gaba (AK Party) da aka kafa ta a ranar 14 ga Agustan 2001, karkashin jagorancin Recep Tayyip Erdogan ta cika shekaru 24 a siyasar Turkiyya, inda ta dinga nasara a dukkan zabukan gama gari da ta shiga.
A bikin cika shekaru 24 na jam’iyyar, Mataimakin Shugaban AK Party, Faruk Acar, ya sanar da cewa za a karbi sababbin mambobi yayin shagulgulan.
Yayin wani taron manema labarai, Acar ya jaddada cewa duk da shekaru 24 da jam’iyyar ta yi, tana nan da kuzari kuma tana ci gaba da bin burinta da manufofinta.
Ya bayyana AK Party ba kawai a matsayin wata jam’iyya ba, amma a matsayin wani gagarumar fafutuka ta jama’a, yana mai cewa, “Watakila ya dace mu bayyana cewa, ba kamar bikin cika shekaru 24 ba, za mu ci gaba da tafiya tare da karfin da muke samu daga jama’a da goyon bayan da muke karba daga al’umma.”
“A karon farko a shekararmu ta 25, za mu shiga wani zangon yakin neman zabe na shekara guda. Manufar wannan yakin neman zabe, wanda zai fara gobe, ita ce mu tafi tare da al’ummarmu kuma mu tunatar da su abubuwan da jam’iyyar da ta kai shekaru 25 ta cim ma a cikin shekaru 25 da suka gabata, inda ta yi tasiri a Turkiyya da miliyoyin ayyuka da shirye-shiryen da ta samar.”
Tun lokacin da aka kafa ta a ranar 14 ga Agusta, 2001, AK Party ta fara jan hankalin jama’a karkashin jagorancin Erdogan, wanda a lokacin shi ne magajin garin birnin Istanbul.
An zabe shi a matsayin Firaminista a shekarar 2003, sannan ya zama Shugaban Kasa tun daga 2014.