Isra’ila ta ce ta kai sama da hare-haren sama 6,000 kan kusan wurare 3,400 a cikin Iran tun bayan harin hadin gwiwa da Amurka da aka fara a ranar 28 ga Fabrairu. Wani babban jami’in sojan Isra’ila ya bayyana cewa hare-haren sun kai ga wuraren soji da kuma wasu muhimman cibiyoyi da ake zargin suna da alaka da karfin makamai masu linzami na Iran.
A cewar jami’in, wadannan hare-haren suna cikin wani babban shiri na rage karfin sojan Iran, musamman domin hana ci gaba ko amfani da makamai masu linzami da za su iya zama barazana ga Isra’ila. Ya kara da cewa hare-haren sun shafi wurare da dama da Isra’ila ke ganin suna da muhimmanci ga tsaronta.
Iran kuwa ta ce ta mayar da martani ta hanyar harba makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuki kan wasu wurare a Isra’ila. Haka kuma ta ce ta kai hare-hare kan wuraren da take zargin suna da alaka da muradun sojan Amurka da Isra’ila a yankin.














