Fashe-fashe sun karaɗe Beirut yayin da Israel ta kai sabbin hare-hare kan birnin da kuma wasu wurare a Tehran. A lokaci guda, wani jirgi mara matuƙi daga Iran ya afka wa tankar mai kusa da filin jiragen sama na Dubai, wanda ya haddasa gobara tare da tilasta dakatar da zirga-zirgar jirage na ɗan lokaci. Ƙasashen Gulf sun ce sun dakile yawancin hare-haren, duk da cewa wasu ɓaraguzai sun sauka a ƙasashensu.
Rikicin ya ƙara tsananta tun bayan hare-haren da Amurka da Isra’ila suka fara kan Iran, inda Tehran ke mayar da martani da harba makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa zuwa Isra’ila da sansanonin Amurka da kuma wasu ƙasashen Larabawa. Haka kuma, ta katse zirga-zirgar jiragen ruwa a Strait of Hormuz, inda kusan kashi ɗaya cikin biyar na man duniya ke bi, lamarin da ya jefa kasuwar makamashi cikin tashin hankali.
Farashin ɗanyen mai ya tashi sosai, inda ya haura dala 100 a kowace ganga, bayan ya kai kusan dala 120 a farkon rikicin. Wannan ya fara jefa matsin lamba ga tattalin arzikin duniya, musamman a ƙasashen da ke dogaro da shigo da mai. A lokaci guda, rahotanni sun nuna cewa daruruwan mutane sun mutu a Iran da Lebanon, yayin da wasu kuma suka jikkata a Isra’ila da sansanonin Amurka.
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya nemi wasu ƙasashe su tura jiragen ruwa domin kare mashigin Hormuz, amma bai samu cikakken goyon baya ba, inda wasu ƙasashe kamar Japan suka nuna rashin shiri. Duk da haka, Trump ya yi gargaɗin cewa Amurka za ta tuna ƙasashen da ba su taimaka ba, yayin da Iran ke jaddada cewa ba ta neman sulhu a wannan lokaci.
Majiyar Labari: NEWSTIMEHUB














