Gwamnatin Nijeriya da Majalisar Dokoki sun goyi bayan tsarin mai da rubuta jarabawar WAEC ta komfuta

Wannan babban sauyin, wanda aka tsara cewa zai fara aiki a shekarar 2026 ya jawo mabambantan ra’ayoyi a tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin ilimi.

Newstimehub

Newstimehub

3 Sep, 2025

3fa13d272ce2dee8b6ecf0e3ce51e44c018d2d69d92f6a1d1bd76a34ec5024c0

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da Majalisar Dokokin Ƙasar sun nuna goyon bayansu kan mayar da rubuta jarabawar kammala sakandare ta Yammacin Afirka, WAEC da komfuta wato CBT.

Wannan babban sauyin, wanda aka tsara cewa zai fara aiki a shekarar 2026 ya jawo mabambantan ra’ayoyi a tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin ilimi.

Amma a yayin da yake jawabi a gaban Majalisar Dokoki da manyan masu ruwa da tsaki a wani taron wayar da kai a Abuja, Ministan Ilimi, Maruf Alausa ya ce jarabawa ta tsarin CBT da za a dinga yi a duka faɗin ƙasar, zai ƙarfafa tsarin ilimin ƙasar.

Alausa ya ce Gwamnatin Tarayya tana goyon bayan rubuta jarabawar WAEC ta komfuta saboda a kawar da satar amsa da kuma tabbatar da an yi sahihiyar jarabawa.

“Mun ɗau aniyar mayar da rubuta jarabawa ta tsarin fasahar komfuta a matsayin wani mataki na samar wa fannin ilimi martaba. A yayin da da fari wasu suka soki wannan sauyi, mun san cewa ba zai yiwu a ci gaba da bin tsarin da aka saba da shi ba.” in ji Minista Alausa.

“An yi wannan tsari ne rubuta jarabawa ta komfuta saboda a rage satar amsa da kare martabar jarabawowinmu. Hakan zai ƙarfafa darajar jarabawowinmu a cikin gida da ma ƙasashen waje.