Ghana ta rufe gidajen rediyo tara kan saɓa ƙa’idojin watsa labarai

Wannan matakin ya biyo bayan wa’adin afuwa na wata guda da shugaban ƙasa John Dramani Mahama ya bayar ga tashoshin da ba su cika ƙa’idoji ba domin gyara kurakuransu na karya dokokin yaɗa shirye-shirye a zangon FM.

Newstimehub

Newstimehub

14 Aug, 2025

1755162959758 wowfsu 0ba24a0c56fa87e924c7f366645bb9ecb73c9fe6db778a7d604bdf41bf0ca18e

Hukumar Sadarwa ta Kasa (NCA) a Ghana ta rufe tashoshin rediyo tara saboda gaza bin ƙa’idojin yaɗa shirye-shirye bayan kwanaki 30 na wa’adin sassauci da shugaban ƙasa ya bayar.

Ministan Sadarwa da Fasahar Zamani na Ghana Sam George ne ya sanar da rufe gidajen rediyon a shafinsa na Facebook.

Wannan matakin ya biyo bayan wa’adin afuwa na wata guda da shugaban ƙasa John Dramani Mahama ya bayar domin bai wa tashoshin da ba su cika ƙa’idoji ba damar gyara kurakuransu na karya dokokin yaɗa shirye-shirye a zangon FM. Sai dai tashoshi shida ba su cika sharuɗɗan da hukumar ta bayar ba kafin ƙarewar wa’adin.

Wannan matakin ya shafi kafafen watsa labarai da dama a faɗin ƙasar waɗanda suka haɗa da: