Faransa ta tsara wani kuɗuri na tsawaita aikin wanzar da zaman lafiya na MDD a Lebanon

Isra’ila da Amurka na adawa da sabunta yarjejeniyar a daidai lokacin da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ke muhawara kan kara wa’adin dakarun wanzar da zaman lafiya a Lebanon har zuwa watan Agustan 2026.

Newstimehub

Newstimehub

20 Aug, 2025

trump un peacekeeping lebanon 93938

Ƙwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya fara muhawara a ranar Litinin kan wani ƙuduri da Faransa ta tsara na tsawaita wa’adin dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD a kudancin Lebanon na tsawon shekara guda da nufin janyewa.

Rahotanni sun bayyana cewa Isra’ila da Amurka na adawa kan sabunta wa’adin rundunar, kuma babu tabbas ko daftarin zai samu goyon bayan Washington, wadda ke da ƙarfin iko a majalisar.

Wani mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ya ce “ba mu ce komai kan tattaunawar da kwamitin sulhu na MDD ke yi ba,” yayin da ake ci gaba da tattaunawa kan makomar dakarun MDD da ke Lebanon (UNIFIL), waɗanda aka tura tun shekarar 1978 don sa ido kan janyewar sojojin Isra’ila bayan sun mamaye Lebanon, da kuma taimaka wa gwamnatin Lebanon wajen mayar da iko a kan iyakar yankin.

Batun, wanda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fara wallafawa, zai “ƙara wa’adin UNFIL har zuwa 31 ga Agustan 2026,” sai dai yana nuna aniyarsa ta yin aiki kan janyewar UNIFIL.”

Hakan zai kbiyo da sharadin cewa gwamnatin Lebanon ce ita kadai” ke samar da tsaro a kudancin Lebanon… da kuma cewa bangarorin sun amince da wani tsari na siyasa.”

Ƙarkashin wata yarjejeniyar da ta kawo ƙarshen yakin baya-bayan nan tsakanin Isra’ila da Hezbollah wadda ke samun goyon bayan Iran, an ci gaba da jibge sojoji a Beirut da kudancin Lebanon tare da wargaza ababen more rayuwa na ƙungiyar a can.

Isra’ila ta ci gaba da kai hari a Lebanon