Danwawu: Gwamnatin Kano ta fara bincike kan kwamishinan da ya karbo belin ‘dilan miyagun ƙwayoyi’

Wannan matakin ya biyo bayan fushin jama’a bayan da aka ga sunan kwamishinan a jikin takardun bayar da belin wanda ake zargin. A halin yanzu gwamnatin jihar ta kafa kwamiti mai mutum bakwai domin gudanar da bincike kan lamarin.

Newstimehub

Newstimehub

26 Jul, 2025

c5d7dd87c2d170b1e889a8d77c5d581b8a8c20c94fc77396fc90d363fb3f9aa0

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya umarci a gudanar da cikakken bincike kan zargin da ke tattare da rawar da Kwamishinan Harkokin Sufuri na Jihar, Alhaji Ibrahim Namadi, ya taka wajen bayar da beli ga wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu.

Wannan matakin ya biyo bayan fushin jama’a bayan da aka ga sunan kwamishinan a jikin takardun bayar da belin wanda ake zargin.

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamna, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar, “Gwamna ya bayar da umarnin a gudanar da bincike mai zurfi dangane da zargin da ke kewaye da bayar da belin wanda ake zargi da safarar miyagun kwayoyi. An kafa kwamitin bincike na musamman domin zurfafa bincike a kan lamarin.”

Kwamitin na da alhakin gano gaskiyar abin da ya faru da bayar da shawarar daukar mataki cikin gaggawa.

Kwamitin yana karkashin jagorancin Barrista Aminu Hussain, mai ba Gwamna shawara kan harkokin Shari’a da Dokoki.

Sauran mambobin kwamitin sun hada da:

  • Barr. Hamza Haladu

  • Barr. Hamza Nuhu Dantani

  • Alhaji Abdullahi Mahmoud Umar

  • Manjo Janar Sani Muhammad (Rtd.)

  • Kwamared Kabiru Said Dakata

  • Hajiya Bilkisu Maimota ce Sakatariyar kwamitin.

    Gwamna Yusuf ya bayyana damuwarsa kan rahoton, tare da jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci wani nau’i na rashin ɗa’a ko tallafa wa ayyukan laifi ba.