Hukumar ƙwallon ƙafa ta Afirka (CAF) ta ayyana Maroko a matsayin wadda ta lashe gasar AFCON 2025 bayan amincewa da ƙarar da ta shigar kan wasan ƙarshe da Senegal.
CAF ta ce an ba Maroko nasara da ci 3-0 ne bayan gano cewa Senegal ta karya dokokin gasar ta hanyar ficewa daga filin wasa yayin wasan ƙarshe.
A wasan da aka buga a Rabat, ‘yan wasan Senegal sun yi zanga-zanga tare da barin filin wasa sakamakon rashin amincewa da hukuncin fenareti da aka yanke.
Hukumar ta danganta hukuncinta da dokoki na 82 da 84, waɗanda ke cewa duk tawagar da ta ƙi ci gaba da wasa za a hukunta ta da kaye kai tsaye.
Wannan hukunci ya bai wa Maroko kofinta na biyu a tarihin AFCON, bayan wanda ta lashe a shekarar 1976, yayin da Senegal ke da damar ɗaukaka ƙara idan ba ta gamsu ba.
Tushen labari: Newstimehub






